ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

by Bello Hamza
2 years ago
Hajjin Bana

A duk shekara, hukumomin kasar Saudiya na bullo da sabbin tsare-tsare don inganta jin dadin Alhazai da kuma yadda ake gudanar da aikin hajjin.

A shekarun baya an fuskanci rushe -rushe domin fadada wurare ibada masu tsarki inda Alhazai musamman ke yin cincirindo domin gudanar da ayyukan ibada.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • A Guji Ajiye Abinci A Firji Fiye Da Kwana 3 – NAFDAC

Rashin issashen wuri ya haifar da mastaloli da dama a shekarun baya inda har aka kai ga rasa rayukan mutane da dama.

ADVERTISEMENT

A wannan shekarar Hukumar Saudi ta bullo da katin tantance mai cikakken izinin kasancewa a wurare masu tsari da ake gudanar da aikin hajji. Katin da aka lakaba wa suna NUSUK ya zama wa wasu mahajjata alakakai, musamman ganin an samu jinkiri daga hukumar Alhazai na ba wasu Alhazai wannan katin, musamman lokacin da aka shigo garin Makkah.

Jami’an tsaron Saudiya sun yi ta kama wadanda ke zirga-zirga ba tare da makale da katin NUSUK a wuyarsu ba. Shiga masallacin harami ya gagari Alhazan da basu da katin NUSUK.

LABARAI MASU NASABA

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

Wannan ya sa hukumar Alhazai ta NAHCON ta kara kaimi wajen ganin ta ba kowa katinsa na NUSUK a kan lokaci.

A bayaninsa na cikakken dalilin bullo da katin NUSUK, wani jami’n tsaro na kasar Saudiya wanda ya nemi mu sakaya sunansa saboda bashi da ikon yin magana da ‘yan jarida, ya ce, a shekarun baya bata gari na shigowa cikin tawagar Alhazai inda suke sace-sace musamman a yayin zaman Muna, Arafat da Muzdalifah, sannan kuma hakan zai taimaka wajen takaita hankoron wadanda basu da izinin gudanar da aikin Hajji shiga wurare masu tsarki inda haka yakan haifar da cunkoso, ga duk wanda ya samu gudanar da aikin hajjin bana zai bayyana maka yadda katin NUSUK ta nastar da shi.

Wannan tsari na NUSUK ya taimaka wajen samun cikakken adadin wadanda suka shigo Saudiya domin aikin hajji da kuma kididdigar daga inda suka shigo. Ma’aikatar aikin Hajji da Umara ta ce, alhazai 1,833,164 suka gudanar da aikin hajjin bana daga sassan duniya sun kuma shigo ne ta hanyoyi daban daban.

Wani abu kuma da ya dauki hankalin duniya gaba daya game da aikin hajjin bana, shi ne irin tsananin zafin ranar da aka yi a ranakun jifar jamra, wanda sai ta kai da hukumar kasar Saudiya, a ta bakin Ministan Umara Hajji Abdulfattah bin Suka bayar da umarnin a dakatar da tafiya jamrat na tsawon awa 5, aka kuma umarci Alhazai su lizimci sha ruwa a kai-kai su kuma guji gararamba a cikin ranar ba tare da wani dalili ba.

Hukumomi su da tabbatar da mutuwar mutum 20 yawancin su daga kasashe yankin nahiyar Asiya.

Duk an kammala aikin Hajjn 2024 hasashe ya nuna cewa, za a ci gaba da fuskantar karin zafin rana inda ake ganin zai iya kaiwa 50 zuwa 60 a ma’aunin zafi.

Hajjin Bana
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.