• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan gudun hijira a Karamar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja sun koka kan yadda ‘yan ta’adda suka mayar da yankinsu sansaninsu na dindindin, inda suka shiga suka yayyanka musu kaji gami da daka sakwara da kuma kwashe kayan abincin da suka tanada a cikin shagunansu.

Da yake zantawa da manema labarai a Kuta kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, Ahmed Almustapha, wani dan gudun hijira daga Rumace-Madalla, ya koka da cewa yayin da suke fama da yunwa a sansaninsu, ‘yan ta’adda sun ci sun cika cikinsu abincin da suka tanada da dabbobinsu.

  • Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa
  • Falalar Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

“Ba mu da jami’an tsaro a cikin al’ummarmu tun bayan janye sojoji daga Allawa. Tun daga wannan lokacin wadannan ‘yan ta’adda sun shafe kwanaki suna kashe mutane fiye da kowane lokaci. ‘Yan fashin sun mayar da yankinmu gidajenssu, su kwana a can suna cin abincin da muka bari a gida. Suna yanka mana kaji su yi miya da su, sannan su cinye mana doya, duk da haka har yanzu ba mai kalubalantar su.

“Tun bayan janyewar wadannan sojoji, mun yi asarar akalla mutu, 50; kuma da yawa an yi garkuwa da su. Makonni uku da suka gabata, an yi garkuwa da mutum 30 a Kauyukan Karaga, Kiriga da Agwaja; kuma har zuwa wannan lokacin, barayin ba su tuntubi kowa ba. Ba mu san inda suke ba ko kuma abin da suke yi da su,” in ji shi.

Rabi’u Iliyasu daga Garin Bassa ya ce duk ‘ya’yansa ba sa zuwa makaranta ne saboda ba shi da wani abin da zai sake daukar nauyin karatunsu.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ya ce, “Duk ’yan uwana suna tare da ni a sansanin. Wasu daga cikin al’ummarmu suna Erena, yayin da wasu suka gudu zuwa sansanin Gwada. Ina tare da matata a sansanin Kuta. ’Yata tana karatau a Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Kuta yayin da wasu kuma suna sauran makarantu. Na janye su ne saboda babu abin da zan daukar nauyin karatunsu.

“Ina da ‘ya’ya 17 da ke tsakanin shekaru 7 zuwa 13 da ke karkashin kulawata, ciki har da marayu da aka kashe iyayensu.

“A halin yanzu, ina wasu kananan ayyuka domin tsira da mutuncina. An yanka mahaifin daya daga cikin yaran da suke tare da ni kwanan nan. An yi garkuwa da mahaifiyar daya daga cikinsu shekaru uku da suka gabata bayan kashe mahaifin; kuma har yanzu ba mu ji komai game da ita ba. ‘Yan bindigar sun bukaci Naira miliyan 3 da babur a matsayin kudin fansa, mun biya su har ma da babur amma ba su sake ta ba. Daga baya mun samu labarin an kashe ta ne bayan an kai musu Naira miliyan uku da babur,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NejaSakwara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Tashin Farashin Wake A Nijeriya

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.