ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kansila

Rundunar ‘yansanda a Jihar Gombe ta kama Kansila mai wakiltar Kumo ta Gabas a Karamar Hukumar Akko da ke jihar Abdullahi Panda da wasu mutum biyu bisa zargin sata da sayar da taransfoma na al’ummar Majidadi.

Da take gabatar da wadanda ake zargin a gaban manema labarai bayan an kama su, kwamishiniyar ‘yansandan Jihar Gombe, Hayatu Usman, ta ce an kama wadanda ake zargin ne bayan da aka samu labarin faruwar lamarin.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Xi Ya Gabatar Da Jawabin Cika Shekaru 70 Na Ka’idoji 5 Na Zaman Tare Cikin Lumana Tsakanin Kasa Da Kasa

Usman ta ce an sayar da taransfomar ce ga wani mai suna Bello Ardo Kumo kan Naira miliyan 1.5, inda ta ce ‘yansanda sun kwato na’urar kuma suna ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin bayan an gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin wadanda ake zargin Hakimin Kauye ne Muhammad Majidadi ya bayyana cewa taransifomar ta shafe shekaru 10 ba ta aiki kuma a lalace take sannan an sace wasu sassanta.

Ya ce al’ummar yankin sun yanke shawarar sayar da taransifomar ce domin gina makarantar Islamiyya da kuma asibiti a kauyen.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Majidadi ta yi ikirarin cewa shi ne ya sanar da kansilan yadda za a yi, amma Panda ya musanta cewa yana da hannu a sayar da taransfomar, ya kuma bukaci a kai maganar kotu.

Bugu da kari, Hukumar Tsaro ta NSCDC, a Gombe, ta gurfanar da wani manomi a kotu bisa daure hannun Adamu dan dan uwansa da ya zarga da laifin sace wayar dansa lamarin da da ya kai ga hannun ya lalace har aka yanke.

Malam Yahaya Buba, mai shekaru 42 da ake tuhuma wanda ya daure hannun dan uwansa Mohammed Adamu mai shekaru 21, ya yi alkawarin bayar da tallafi mara iyaka ga wanda aka yanke masa hannu.

An ruwaito cewa hannayen Adamu sun yi rauni, bayan da aka daure na tsawon sa’o’i, lamarin da ya hana zagayawar jini daga sauran sassan jikinsa zuwa hannayen, wanda hakan ya jawo illa gare shi.

Tun da farko, Buba, wanda kawun Adamu ne, ya zargi dan uwansa, Adamu, da satar wayar dansa.

Buba, wanda manomi ne kuma mai wayar da kan jama’a, ya dora laifin afkuwar lamarin kan aiki ne na shaidan, inda ya ce dama kuma Adamu ya taba yin sata.

Wanda ake zargin ya bayyana cewa, “Ni manomi ne daga Sambo Daje a Kashere, Masarautar Pindiga, Karamar Hukumar Akko. Na shuka masara da wake, wanda nake nomawa, ina da ‘ya’ya 10, amma biyu sun mutu a halin yanzu ina da ‘ya’ya takwas da suka rage da mata daya.

“Shi (Adamu) ya kasance yana shiga gidajen mutane don yin fashi, yana satar kayayyaki kamar awaki, shanu, da amfanin gona.

“A duk lokacin da ya saci amfanin gona misali, in buhu daya ya sata sai ya kona sauran amfanin, sanna a duk lokacin da aka kama shi suka gaya min na kan roki gafararsu su bar shi ni a yi min horo,” in ji Buba

Da yake tsokaci a kan dalilin da ya sa ya zabi daure hannunsa a matsayin hukunci, Buba ya zargi kansa da daukar doka a hannunsa “Yaron ya sace wayar dana sai wani mutum ya kama shi aka kawo shi gida, muka daure shi a gida tun daga 1:30 har zuwa lokacin da aka sakko daga Sallar jumma’a.

Muka bar yaron a daure a gida. Kuskuren da na yi shi ne lokacin da aka kawo mini yaron, na dauki doka a hannuna maimakon in nemo hanyar da ta dace,” kamar yadda ya zargi kansa.

Da yake karin haske game da irin hukuncin da aka yi wa Adamu, Buba ya ce, “Da farko na yi niyyar kwance shi kafin in tafi Sallah amma saboda ina da shakkar yaron zai gudu shi ya sa na bar shi daure da misalin karfe 1:30 na rana, ban kwance shi ba sai misalin karfe 2:15 na wannan rana. Shirina shi ne in kai shi sashen ‘yansanda na Kashere, amma hakan ya gagara saboda fushina.

Yayin da ya yaba da kokarin jami’an tsaron Nijeriya da jami’an tsaron NSCDC na shiga cikin lamarin,

“Iyayen (Adamu) wanda aka abin ya faru da shi, bayan sun ji abin da ya faru da dansu, sun kai karar ofishin hukumar tsaro ta Cibil Defence suna neman hakkin dan nasu kuma dole ne a hukunta ni. Amma da na isa ofishin, sai aka ce in fara biyan Naira 30,000 na jinyar yaron kuma in sa hannu a kan cewa zan dauki alhakin duk abin da zai faru da yaron nan gaba.

“Na biya kudin, sannan dan uwana (mahaifin Adamu) ya karbi kudin ya tafi, kuma na ci gaba da biyan kudin jinyar yaron duk da na biya Naira 30,000 na farko.

“Ina so in gode wa NSCDC saboda yin la’akari da lamarin. Duk da cewa suna tuhuma ta amma sun yi kokari sosai wajen gyara lamarin.

“Watakila da a ce sun shiga lamarin tun da farko da ba a kai ga yanke masa hannu ba, amma dai sun tabbatar da lafiyar yaron, sun sanya hannu a kan duk takardun da suka dace don ganin yaron ya samu kyakkyawar kulawa,” in ji Buba.

Ya ci gaba da jaddada cewa, “Duk da haka, jami’an NSCDC, sun tabbatar da cewa Adamu ya samu mafi kyawun kulawar jinya,” in ji shi.

Adamu, wanda ya musanta zargin kawun nasa, ya ce a tarinisa bai taba sata ba.

Da aka tuntubi mahaifin Adamu, Tela Daji, ya musanta zargin da Buba ya yi masa na yin almubazzaranci da kudin da aka tanadar domin jinyar dansa.

“Yayana yana kokarin nemo wanda zai zarga da yadda zai wanke kannsa a cikin lamarin.

“Ban dauki wani kudi da aka tanadar ba. Hasali ma lokacin da aka bayar da Naira 100,000 ba ni ne aka ba wa. NSCDC ce ta kasance mai kula da harkar maganin, ban taba barin wurin da dana yake ba,” in ji shi.

A halin da ake ciki, Hukumar NSCDC ta fara tuhumar Buba da laifin aikata laifuka, kamar yadda ta yi alkawari a wata hira da Kwamanda Muhammad Bello, da wakilinmu.

Sai dai bisa ga bayanan kotu da Arewa PUNCH ta samu, an dakatar da shari’ar saboda Buba ba shi da wakilci a shari’ar.

Mai shari’a Durabo Sikam na babbar kotun Gombe a ranar 9 ga watan Yuli ya sanya ranar 8 ga watan Yuli domin gurfanar da shi a gaban kuliya.

Magatakardar Kotun, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, “Dalilin da ya sa aka dakatar da shari’ar a halin yanzu shi ne saboda wanda ake kara (Buba) ya bukaci kotu da ta ba shi wasu kwanaki domin ya samo lauyan da zai kare shi.

Kansila
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Iyayen Yaron Da Aka Kashe A Makarantar Sojin Sama Sun Bukaci A Yi Adalci

Iyayen Yaron Da Aka Kashe A Makarantar Sojin Sama Sun Bukaci A Yi Adalci

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.