• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayen Yaron Da Aka Kashe A Makarantar Sojin Sama Sun Bukaci A Yi Adalci

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Iyayen

Iyalan marigayi mataimakin shugaban daliban makarantar sakandare ta Rundunar Sojin Sama da ke Kaduna, Felid Blaise, wanda ake zargin wasu daliban aji shida (SS3) ne suka kashe a dakin kwanan makarantar sun yi kira da a yi musu adalci. 

Wani daga cikin kawunnen marigayin mai suna Paul ya magantu game da mutuwar marigayin dalibin wanda kuma shi ya bukaci yin adalcin.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Wani Alhaji Ya Sake Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta A Makkah

Mista Paul ya ambata wannan bukata ne a Kaduna a lokacin da yake zantawa da manema labarai inda ya bayyana cewa marigayi Felid kanensa ne kuma maraya da ya rasa iyayensa biyu a shekarar 2013.

Ya ci gaba da cewa, abin da ya fi dacewa da mahukuntan makarantar da rundunar sojojin saman Najeriya (NAF) za su iya yi don karrama marigayin shi ne kara kaimi wajen bankado abin da ya kai ga mutuwarsa.

Ya bayyana cewa ya ga marigayi Felid cikin koshin lafiya a lokacin da ya ziyarce shi a yayin hutun Sallah, ya kara da cewa mutuwar yaro haziki kuma mai tarbiyya ya jefa kansa da iyalansa baki daya cikin dimuwa.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Ya ce sakataren ilimi na sansanin sojin sama ne ya sanar da iyalan rasuwar dan uwansu.

“An tabbatar mana da cewa a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don zakulo wadanda suka aikata laifin da kuma ganin an yi adalci.

“Mu a matsayinmu na danginsa mun amince da amincin makarantar da kuma rundunar sojojin sama, kuma muna da yakinin cewa wadanda suka kashe danmu ba za su tsira daga hukunci ba,” in ji Paul.

Rundunar sojin saman Najeriya ba ta bayyana sunan wanda aka kashe da kuma musabbabin mutuwarsa ba, amma ta sanar da cewa a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da kwakkwaran bincike domin gano abin da ya kai ga mutuwarsa.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin Rundunar, Air Bice Marshal Edward Gabkwet, a wata ‘yar gajeriyar sanarwa da ya fitar ya ce, “Shugaban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar, da daukacin jami’an NAF na cike da alhini wannan lamari mai radadi da bakin ciki da ya faru na mutuwar daya daga cikin dalibanmu a makarantar sakandaren sojojin sama, Kaduna.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

LABARAI MASU NASABA

Iyayen

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.