ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayen Yaron Da Aka Kashe A Makarantar Sojin Sama Sun Bukaci A Yi Adalci

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Iyayen

Iyalan marigayi mataimakin shugaban daliban makarantar sakandare ta Rundunar Sojin Sama da ke Kaduna, Felid Blaise, wanda ake zargin wasu daliban aji shida (SS3) ne suka kashe a dakin kwanan makarantar sun yi kira da a yi musu adalci. 

Wani daga cikin kawunnen marigayin mai suna Paul ya magantu game da mutuwar marigayin dalibin wanda kuma shi ya bukaci yin adalcin.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Wani Alhaji Ya Sake Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta A Makkah

Mista Paul ya ambata wannan bukata ne a Kaduna a lokacin da yake zantawa da manema labarai inda ya bayyana cewa marigayi Felid kanensa ne kuma maraya da ya rasa iyayensa biyu a shekarar 2013.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa, abin da ya fi dacewa da mahukuntan makarantar da rundunar sojojin saman Najeriya (NAF) za su iya yi don karrama marigayin shi ne kara kaimi wajen bankado abin da ya kai ga mutuwarsa.

Ya bayyana cewa ya ga marigayi Felid cikin koshin lafiya a lokacin da ya ziyarce shi a yayin hutun Sallah, ya kara da cewa mutuwar yaro haziki kuma mai tarbiyya ya jefa kansa da iyalansa baki daya cikin dimuwa.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ya ce sakataren ilimi na sansanin sojin sama ne ya sanar da iyalan rasuwar dan uwansu.

“An tabbatar mana da cewa a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don zakulo wadanda suka aikata laifin da kuma ganin an yi adalci.

“Mu a matsayinmu na danginsa mun amince da amincin makarantar da kuma rundunar sojojin sama, kuma muna da yakinin cewa wadanda suka kashe danmu ba za su tsira daga hukunci ba,” in ji Paul.

Rundunar sojin saman Najeriya ba ta bayyana sunan wanda aka kashe da kuma musabbabin mutuwarsa ba, amma ta sanar da cewa a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da kwakkwaran bincike domin gano abin da ya kai ga mutuwarsa.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin Rundunar, Air Bice Marshal Edward Gabkwet, a wata ‘yar gajeriyar sanarwa da ya fitar ya ce, “Shugaban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar, da daukacin jami’an NAF na cike da alhini wannan lamari mai radadi da bakin ciki da ya faru na mutuwar daya daga cikin dalibanmu a makarantar sakandaren sojojin sama, Kaduna.”

Iyayen
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.