• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)

by Idris Aliyu Daudawa
11 months ago
in Ilimi
0
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan na karanta wani rahoto mai ban sha’awa da ya yi bayani a kan yadda karancin malaman darussan turanci da lissafi ke kassara samun ilimi mai inganci daga tushe.

Abokin aikina da ya rubuta rahoton, Samuel Abulude ya zakulo matsalolin da suke addabar ilimi da kuma kwazon dalibai a makarantun Firamare da Sakandare a Nijeriya, inda ya dora alhakin lamarin a kan karancin Malaman Turanci da na Lissafi a makarantun fadin tarayyar Nijeriya.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Wani Alhaji Ya Sake Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta A Makkah

Ba abin da za a boye ba ne batun rashin ingancin ilimi a Nijeriya, domin kuwa a shekarun da suka gabata; kasafin kudi na shekara-shekara na gwamnatocin tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi, ya yi matukar raguwa, musamman idan aka duba shawarar kason da majalisar dinkin duniya da hukumominta suka ba da shawarar a rika ware wa sashen na ilimi.

Hukumar ilimi, kimiyya da al’adu ta majalisar dinkin duniya (UNESCO), ta ba da shawarar mambobin hukumar su ware kashi shida na kudaden da suka shigo ko kuma kashi 15 zuwa 20 na kasafin kudin shekara, domin tallafa wa ilimi. Sai dai kamar yadda hukumar ta UNESCO ta bayyana, “Yawancin kasashe har zuwa yanzu ba su aiwatar da wannan shawara da aka ba su ba, wadda za ta taimaka wajen bunkasa ilimi”.

Mafi yawancin manyan makarantun Firamare da Sakandare na fama da wadannan matsaloli, yayin da hukumomin da wadanda abin ya shafa suka yi buris da al’amarin, misali kamar hukumomin Jami’o’i na kasa da kuma na ilimin bai-daya.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

Har ila yau, hukumar ilimin bai-daya ta shirya taron kara wa juna sani na tsawon kwana biyu, wanda ya hada kwamitin ilimi na majalisar dattawa da jami’an ma’aikatar ilimi ta kasa, a kan wannan karanci na malaman Turanci da Lissafi, wanda kai tsaye ke shafar ingancin ilimi a dukkanin fadin Nijeriya.

A makarantun sakandare, ana ci gaba da fuskantar wannan matsala ta rashin ingancin koyarwa, wanda hakan ke matukar shafar dalibai tare da yi musu tasiri a rayuwarsu.

Babu shakka, wannan matsala ta zama ruwan dare shekara da shekaru, wanda hakan ya kan yi tasiri matuka a kan matasa masu tasowa a halin yanzu. Duk irin abubuwan da suka koya, walau masu kyau ko akasin haka; na iya yin tasiri a rayuwarsu, domin suna kan wata gaba ce ta zama manyan gobe.

A irin wannan yanayin ne, ake koya musu yadda za su rika yin karatu, ya kasance kuma karatun yana shiga kwakwalwarsu da yadda za su ci abinci da kuma yadda za a reni kwazonsu ta hanyar yin la’akari da yadda suke, sannan da kuma yadda za su kyamaci yin ta’ammali da miyagun kwayoyi da dai sauran makamantansu.

Wata mai makaranta mai zaman kanta a Minna, Jihar Neja Olamide Alalade, ta yi magana ne dangane da lamarin inda ta ce, “batun rashin malaman Lissafi da na Turanci a makarantu, na da alaka ne kai tsaye da rashin daukar matakan da suka kamata a dauka. A cewar tata, kamata ya yi mu sake yin tunani kan yadda zamu rika tafiyar da al’amuranmu kamar yadda sauran kasashen waje ke tafiyar da nasu a kan wannan harka ta ilimi”.

Da take yin karin bayani Alalade cewa ta yi, al’umma na yi wa harkar ilimin rikon sakainar kasha, ko kuma sha yanzu magani yanzu, maimaikon daukar matakan da suka dace; wadanda za su taimaka wajen cin moriyar al’amarin kwarai da gaske.

Magana ta gaskiya ita ce, gwamnati da sauran al’umma ya kamata su bada gudunmawar da ta dace, musamman wajen bayar da gudunmayar kudade, domin ilmantar da ‘ya’yansu.Ta ce, “koma me al’umma suka yi; indai bat a da niyyar sa kudade da yawa a wannan bangare na ilimi; a nan gaba, wato shekaru masu zuwa babu wani abin kirki da za a sa ran gani, domin duk wasu abubuwan da aka fara ba za a dauke su da muhimmanci ba, illa ma daga karshe a samu sun lalace’’.

Hadin Sabulu Na Musamman


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

Next Post

Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

Related

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu
Ilimi

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

5 hours ago
Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

2 weeks ago
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Ilimi

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

2 weeks ago
Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje
Ilimi

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)
Ilimi

Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)

4 weeks ago
Next Post
Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.