• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Sojoji Ba Za Su Yi Wa Dajin ‘Yan Ta’adda Ruwan Bama-bamai Ba – Gwamnati

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Abin Da Ya Sa Sojoji Ba Za Su Yi Wa Dajin ‘Yan Ta’adda Ruwan Bama-bamai Ba – Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne fadar shugaban kasa ta bayyana dalilin da ya sa ba za ta iya ruwan bama-bamai a dajin da aka yi garkuwa da fasinjojin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ba, inda ta ce yin hakan zai kashe wadanda ba su ji ba ba su gani ba, laifinsu kadai shi ne hawa jirgin kasa.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin da yake maida martani kan wani sabon faifan bidiyo da ‘yan ta’addan jirgin kasan suka fitar, inda suka yi barazanar kashe wasu daga cikin fasinjojin tare da yin garkuwa da shugaban kasa Muhammadu Buhari da Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El Rufa’i idan ba a gaggauta biya musu bukatunsu ba.

  • Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

A cikin sanarwar, Garba Shehu ya ce jami’an tsaro na kasar nan ba ragwaye ba ne, amma ‘yan ta’addan na kokarin amfani da farfaganda ne don tilasta wa gwamnati su amince su mika wuya ga bukatunsu na siyasa – wannan dabaru ne wadanda an saba ganin su a duk fadin duniya.

A cewarsa, jami’an tsaro na da tsare-tsare da dabarunsu wajen yaki da ta’addanci wadanda ba zai yiwu a dinga nuna su a kafafen yada labarai ba.

Shehu ya kara da cewa yin amfani da sojojin sama wajen tayar da bama-bamai a Dajin da ‘yan ta’addan suke, zai halaka mutanen da gwamnati da ‘yan Nijeriya ke son ceto wa da ransu.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ta Kashe Kanta Bayan Kone Mijinta Bisa Zargin Cin Amana

Next Post

Zamu Hukunta Duk Wanda Ba Musulmin Ba Da Ya Sake Keta Harami – Saudiyya

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

4 weeks ago
Sojoji
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

1 month ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 month ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 months ago
Next Post
Zamu Hukunta Duk Wanda Ba Musulmin Ba Da Ya Sake Keta Harami – Saudiyya

Zamu Hukunta Duk Wanda Ba Musulmin Ba Da Ya Sake Keta Harami - Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

July 9, 2025
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

July 9, 2025
An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

July 9, 2025
EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

July 9, 2025
An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

July 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

July 9, 2025
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

July 9, 2025
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

July 9, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

July 9, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.