• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPC Ta Sanya Dokar Ta Ɓaci A Fannin Haƙo Mai

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Tattalin Arziki, Manyan Labarai
0
NNPC Ta Sanya Dokar Ta Ɓaci A Fannin Haƙo Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin man fetur na ƙasa (NNPCL) ya kafa dokar ta-baci kan haƙo mai da iskar gas a Nijeriya, tare da yin kira da a haɗa kai tsakanin masu ruwa da tsaki domin tunkarar kalubalen a fannin. 

A yayin taron baje kolin mai da iskar gas na Nijeriya karo na 23 da aka yi a Abuja, babban jami’in gudanarwa na ƙungiyar Engr. Mele Kyari ya jaddada buƙatar ɗaukar ƙwararan matakai domin shawo kan matsalolin da ke hana hako danyen mai yadda ya kamata.

Kyari ya yi nuni da cewa, idan aka kula da kuma ɗaukar matakan da ya dace, Nijeriya za ta iya haƙo ganga miliyan biyu na ɗanyen mai a kowace rana idan aka zuba jari da sabbin na’urori, amma rashin inganci da tsaikon sayo wa ke kawo cikas ga ci gaba.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Kar Ku Tayar Da Hankulanku, Mun Samo Fetur Fiye Da Lita Biliyan 1.5 – NNPCL

Kyari ya bayyana cewa, hukumar ta NNPC da abokan hulɗarta za su magance waɗannan ƙalubale ta hanyar ɗaukar matakai kamar maye gurbin tsohon bututun ɗanyen mai da kuma aiwatar da shirin raba rigima domin kula da na’urorin da ake haƙowa a ƙasar nan na tsawon shekaru huɗu zuwa biyar.

Ya bukaci masu ruwa da tsaki da masana’antu da su yi aiki tare don rage farashin samarwa da haɓaka kayan aiki zuwa matakan da aka ƙuduri niyya. Bugu da kari, Kyari ya bayyana ƙudirin NNPCL na saka hannun jari a muhimman kayan aiki na iskar gas, kamar su Obiafu-Obrikom-Oben (OB3) da bututun iskar gas na Ajaokuta-Kaduna-Kano (AKK), don bunƙasa samar da iskar gas a cikin gida da samar da wutar lantarki da ci gaban masana’antu.

Labarai Masu Nasaba

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GasKyariNNPCOil
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilai Ta Fara Shirin Ƙirƙirar Wata Sabuwar Jiha a Kudu

Next Post

Tinubu Ya Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Babban Ɗan Jarida Kabir Yusuf

Related

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

3 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

5 hours ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

9 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

11 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

1 day ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

1 day ago
Next Post
Tinubu Ya Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Babban Ɗan Jarida Kabir Yusuf

Tinubu Ya Miƙa Saƙon Ta'aziyyar Babban Ɗan Jarida Kabir Yusuf

LABARAI MASU NASABA

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

July 2, 2025
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

July 2, 2025
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

July 2, 2025
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.