• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
11 months ago
in Ilimi
0
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

…shi ma da ya tofa nasa albarkacin bakin dangane da rash-in albashi mai tsoka, Olamide Alalade ya yi kira ga masu ruwa da tsaki wajen tafiyar da al’amuran ilimin daga kowane bangare, da su samar da albashi mai tsoka; wan-da zai iya magance matsalolin da malaman makaranta ke fuskanta na rayuwar a halin yanzu.

Alalade ya kara da cewa, akwai bukatar a kara mayar da hankali a kan makarantun da suke a kauyuka, birane da kuma sauran wuraren da ke makwabtaka da su. “

  • Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)
  • Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)

Malaman da muke da su yanzu, na wucin-gadi ne; mu-samman a bangaren Turanci da Lissafi, hakan ne zai sa ba za mu taba hada tsakanin malaman da suke na dindindin da kuma na wucin-gadi ba, ko da kuwa a kwazon su kansu daliban; domin za su fi mayar da hankali idan suna da malamai na dindindin.

Me yasa muke da malaman wucin gadi a bangaren Tu-ranci da Lissafi a makarantu? Amma, sai ga shi muna ganin malamai da dama na neman koyarwa ta wucin ga-din, saboda irin wadannan malaman ba su da lokacin da za su bayar wajen taimaka wa daliban, su gane wuraren da suke da matsaloli; domin su gyara. Idann ana ma-ganar malaman wucin gadi, dole ne malamai su raba hankalinsu wajen suntiri daga wannan makaranta zuwa waccan makaranta, ko kuma su fara tunanin yin wata sa-na’a daban. Abu mafi kyau shi ne a samu malaman Lissa-fi da Turanci wadanda za su kasance a makaranta a kowane lokaci, domin taimaka wa ‘ya’yanmu dalibai wajen inganta iliminsu a cewar Alalade.

Yadda Makarantun Suka Bambanta

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Bugu da kari, Alalade ya ce; yadda makarantu suka bam-banta kan lamuransu, na shafar irin hazakar da daliban suke da ita ko samu daga makarantun. Yayin da kuma wasu makarantu ke kallon irin ribar da za su samu, wasu kuma ilimin da daliban za su samu shi ne damuwarsu.

“Idan makarnta ta kasance ba ta da wasu muhimman lamuran da ta sa a gabanta, musamman na koyar da da-russa, sai ya kasance malaman za su mayar da hanka-linsu ne a kan wasu dalibai a cikin ajin kawai, su kuma manta da sauran. Mun kuma lura da cewa, idan yara ma-su zuwa makaranta suka karu, a nan ba ana nufin ana karuwa ba ne da ilimi.

Malamai kalilan ne, amma ana amfani da su wajen koya wa dalibai da dama karatu. Shin akwai wasu matakai ko kididdigar da ke nuna cewa, a duk shekara ga yawan wadanda suka karanta fannin koyarwa; wadanda za su tafiyar da irin bukatar da ake da ita a Nijeriya?

Abin ba haka yake ba, muna dai da makarantun da suka kasance wurin da ake amfani da malaman da ba su can-canta ba. Ba da dadewa ba, aka samu irin wannan lamari wanda ya dace a ce an dauki babban mataki,  akwai kashi 50 na wadanda suka rubuta jarrabawar shiga manyan makarantu (Jamb), wadanda suka samu maki kasa da 200; saboda wasu makarantun na tafiyar da harkokin nasu ne kawai, don samun riba maimakon ganin daliban nasu na yin fice wajen samun nasarar jarabawar.

Kamata ya yi mu rika kaucewa kaskantar da samun ci gaban ilimi, saboda ba mu da wadanda suka cancanta su kasance a guraben da ake so. Kamata ya yi samar da mu-radin yin gyara, ba ya kasance jiya tafi yau ba. Mutane ba za su ga muhimmancin abin da aka yi watsi da shi ba!

 

Ba A Kallon Aikin Koyarwa Da Muhimmanci

A ganin Omisore, akwai bukatar kwarewa idan har ana maganar malamai masu nagarta, wadanda za su dora dalibai a tudun mun tsira na harkar koyon karatu.

“Ya ce,  a ganinsa dalili na biyu shi ne yadda lamarin ko-yarwa ya lalace tare da tabarbarewa, daya daga cikin abubuwan da yake amfani da su a matsayin dabarun ho-rarwa, don samun nasarar aikin koyarwa da suka hada da A, B, C, D da E. A, malami ya tafiyar da kai a duk halin da ya samu kansa, B ya iya mu’amala da al’umma, C can-cantar yin aikin, D sanin hanyar koyarwar da ta dace, E sabo da aikin saboda yau da kulllum.

Cancanta ita ce tafi komai muhimmanci ga malami, mu-samman wajen cimma burin koyarwar, yawancin mala-mai ba sa bin hanyoyin da za su kara inganta kansu, daga karshe suna dora dalilin hakan a kan rashin albashi mai tsoka.

Dalili na uku, na da alaka da na daya da biyu, wanda gaba daya yana da nasaba da yadda aka yi wa lamarin rikon sakainar kashi, wato aikin koyarwa, saboda rashin can-canta da kuma yadda ake yi wa aikin koyarwar kallon masheka Aya. Haka nan, ma ana iya samun Kwalejin ilimi an cika ta da daliban da ba su samu damar cancanta a dauke su ba, ba domin komai ba sai saboda wadanda su-ka cancanci ba su da sha’awar lamarin da ya shafi ko-yarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: shugabannin ArewaSiyasar ArewaTabarbarewar Ilimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fahimtar Manufar Kasar Sin Ta Yin Kwaskwarima A Sabon Zamani

Next Post

Peng Liyuan Ta Yi Kira Da Karin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasa Da Kasa Domin Takaita Cututtukan Kanjamau Da Tarin Fuka

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

6 days ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

1 week ago
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
Ilimi

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

1 week ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

2 weeks ago
Next Post
Peng Liyuan Ta Yi Kira Da Karin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasa Da Kasa Domin Takaita Cututtukan Kanjamau Da Tarin Fuka

Peng Liyuan Ta Yi Kira Da Karin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasa Da Kasa Domin Takaita Cututtukan Kanjamau Da Tarin Fuka

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
turanci

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.