• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Nijeriya Ba Daga APC Ba Ce – Gwamna Uzodimma

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki ta APC ta yi iya bakin kokarinta wajen ciyar da kasar nan. Ya ce kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a kasar nan duka a duniya ne.

Uzodimma, wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin APC (PGF), ya bayyana haka a Abuja lokacin da ya jagoranci zababbun gwamnonin jam’iyyar APC a ziyarar da suka kai wa shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, wanda yake jagorantar kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki.

  • 2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC
  • Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Gwamnan ya ce, “Gaskiyar magana ita ce, jam’iyyar APC ta yi kokari sosai a Nijeriya. Abin da ke faruwa a halin yanzu matsalar ce na tattalin arzikin duniya baki daya.

“Mu a Nijeriya karkashin jagorancinmu na Shugaban kasa, Bola Tinubu mun fitar da tsare-tsare don magance matsin tattalin arziki, idan aka yi la’akari da irin tattalin arzikin da yake ciki duba da irin yanayin da ya samu kansa. Ina da yakinin cewa nan ba da dadewa ba ‘yan Nijeriya za su dara.”

Dangane da damar da jam’iyyar take da shi na samun nasara a zaben gwamnonin Edo da Ondo duba da halin kuncin da kasar nan ke ciki, Uzodimma ya ce jam’iyyar APC ce ke rike da jihohi 20 cikin 30 na kasar nan, tare da shugabancin kasa, kuma idan har zabe abu ne wanda yake tattare da wayan jama’a, lallai masu rinjaye ne za su samu shugabanci.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

A nasa bangaren, Ganduje ya ce shugabannin jam’iyyar za su yi kokarin kulla kyakkyawar alaka da gwamnoni a karkashin tutar jam’iyyar APC.

Ya ce, “Babu shakka mun yi matukar farin ciki a yau da na samu labarin kuna zuwa. Don haka, ina ganin wannan wata ni’ima ce mai girma a gare mu. Saboda haka, mun yi farin ciki da wannan ziyara kuma muna da kwarin gwiwa a kanku.

“Za mu yi duk mai yiwuwa don ganin mun ci gaba da wanzar da kyautata alaka da gwamnoninmu a fadin kasar nan, kuma za mu taimaka wajen kare muradunsu wanda ko shakka babu su ma suna taimaka wa jam’iyyar, suna sa jam’iyyar ta yi kara armashi kamar yadda ya kamata.”

Uzodinma ya kasance tare da Gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Out da Gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa da takwaransu na Jihar Ekiti, Abiodun Oyebanji a wurin wannan ziyara


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ingila Da Spain Wa Zai Yi Nasara A Berlin?

Next Post

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje – Kungiyar Dalibai

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
manja

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje - Kungiyar Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.