• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Nijeriya Ba Daga APC Ba Ce – Gwamna Uzodimma

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki ta APC ta yi iya bakin kokarinta wajen ciyar da kasar nan. Ya ce kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a kasar nan duka a duniya ne.

Uzodimma, wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin APC (PGF), ya bayyana haka a Abuja lokacin da ya jagoranci zababbun gwamnonin jam’iyyar APC a ziyarar da suka kai wa shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, wanda yake jagorantar kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki.

  • 2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC
  • Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Gwamnan ya ce, “Gaskiyar magana ita ce, jam’iyyar APC ta yi kokari sosai a Nijeriya. Abin da ke faruwa a halin yanzu matsalar ce na tattalin arzikin duniya baki daya.

“Mu a Nijeriya karkashin jagorancinmu na Shugaban kasa, Bola Tinubu mun fitar da tsare-tsare don magance matsin tattalin arziki, idan aka yi la’akari da irin tattalin arzikin da yake ciki duba da irin yanayin da ya samu kansa. Ina da yakinin cewa nan ba da dadewa ba ‘yan Nijeriya za su dara.”

Dangane da damar da jam’iyyar take da shi na samun nasara a zaben gwamnonin Edo da Ondo duba da halin kuncin da kasar nan ke ciki, Uzodimma ya ce jam’iyyar APC ce ke rike da jihohi 20 cikin 30 na kasar nan, tare da shugabancin kasa, kuma idan har zabe abu ne wanda yake tattare da wayan jama’a, lallai masu rinjaye ne za su samu shugabanci.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

A nasa bangaren, Ganduje ya ce shugabannin jam’iyyar za su yi kokarin kulla kyakkyawar alaka da gwamnoni a karkashin tutar jam’iyyar APC.

Ya ce, “Babu shakka mun yi matukar farin ciki a yau da na samu labarin kuna zuwa. Don haka, ina ganin wannan wata ni’ima ce mai girma a gare mu. Saboda haka, mun yi farin ciki da wannan ziyara kuma muna da kwarin gwiwa a kanku.

“Za mu yi duk mai yiwuwa don ganin mun ci gaba da wanzar da kyautata alaka da gwamnoninmu a fadin kasar nan, kuma za mu taimaka wajen kare muradunsu wanda ko shakka babu su ma suna taimaka wa jam’iyyar, suna sa jam’iyyar ta yi kara armashi kamar yadda ya kamata.”

Uzodinma ya kasance tare da Gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Out da Gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa da takwaransu na Jihar Ekiti, Abiodun Oyebanji a wurin wannan ziyara


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ingila Da Spain Wa Zai Yi Nasara A Berlin?

Next Post

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje – Kungiyar Dalibai

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

6 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

6 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

6 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

4 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

4 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

1 month ago
Next Post
manja

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje - Kungiyar Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.