• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Cire Rubutun Ajami A Kudin Nijeriya

by Sadiq
11 months ago
in Labarai
0
Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Cire Rubutun Ajami A Kudin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun tarayya da ke Jihar Legas, ta yi watsi da wata kara da aka shigar gabanta na neman cire rubutun ajami a takardun kudin Nijeriya.

Barista Malcolm Omirhobo ne ya shigar da karar, inda yake kalubalantar Babban Bankin Nijeriya (CBN), kan kotu ta umarce shi domin cire rubutun ajami na harufan Larabci daga takardar Naira.

  • Southgate Ya Ajiye Aikin Horas Da Ingila
  • An Kaddamar Da Harkar Sada Zumunta A Tsakanin Yaran Sin Da Na Afirka

Kotun ta yi watsi da karar a ranar Talata, inda mai shari’a Yellim Bogoro, ya nuna cewa wanda ya shigar da karar ya gaza bayar da hujjoji da za su nuna cewa CBN ya sanya rubutun ajami da wata mummunar manufa.

Kafin zartar da hukuncin, kotun ta ce Nijeriya kasa ce mai cikakken ‘yanci, inda ya jaddada da cewa babu fifita wani addini ko kabila.

Tun a 2020 aka fara shari’ar, wanda sai a yau Talata babbar kotun da ke Lagos ta zartar da hukunci.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Mai shari’a Yellim, wanda ya yi watsi da karar ya kara da cewa kotun ta dogara ne da shari’ar Cif Gani Fawehinmi da Akilu da aka yi a shekarar 1998.

Kotun ta ce yayin da Cif Omirhobo ke da gurbi don sauraron kararsa amma kuma ya kasa bayar da isasshiyar hujja da za ta nuna cewa tsarin da CBN ya yi don ci gaba da amfani da rubutun ajami kan takardun Naira da rubutun Larabci, an yi shi ne da muguwar manufa.

Sauran wadanda suke cikin shari’ar sun hada da kungiyar kare hakkin Musulmi karkashin daraktanta, Farfesa Ishaq Akintola da kuma Umar Kalgo, wani fitaccen lauya mazaunin Jihar Kebbi.

Babban Daraktan kungiyar kare hakkin Musulmi , Farfesa Ishaq Akintola, bayan yanke hukuncin ya ce wannan nasara ce mai cike da albishir ga Musulmi da masoya Musulunci a fadin Nijeriya.

A martanin da ya mayar kan hukuncin, Mista Omirhobo ya ce ya nemi a ba shi kwafin hukuncin kuma zai yi nazari don daukar mataki na gaba.

Da yawa dai ba su fahimci cewa kafin zuwan turawan mulkin mallaka galibi ana amfani ne da harufan Larabci domin rubuta harsunan Afirka da ake kira “Ajami.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjamiKotuLegasRubutuTakardun Naira
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya 15 Ne Suka Rasu A Hajjin Bana – NAHCON

Next Post

Kwalara Ta Hallaka Mutane 103, Mutane 3000 Sun Kamu A Nijeriya 

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

49 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
Kwalara Ta Hallaka Mutane 103, Mutane 3000 Sun Kamu A Nijeriya 

Kwalara Ta Hallaka Mutane 103, Mutane 3000 Sun Kamu A Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.