• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: NLC, ASUU da Sauran Kungiyoyi Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Zanga-zanga

Kungiyar Kwadago Ta Kasa reshen Jihar Kebbi (NLC), tare da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da sauran kungiyoyi sun gudanar da zanga-zangar lumana a manyan titunan birnin Kebbi, a jihar Kebbi kan goyon bayan yajin aikin da ASUU ke yi.

Karkashin jagorancin shugaban kungiyar NLC reshen jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhasaan, masu zanga-zangar dauke da rubuce-rubuce daban-daban, kamar “kawo karshen yajin aikin ASUU yanzu, rufe jami’o’i yana da illa ga tattalin arziki, siyasa, likitanci, al’umma da shari’a.

  • Zaben Fidda-Gwanin PDP: Kotu Ta Fara Sauraren Karar Dan Majalisar Argungu/Augie a Kebbi
  • NNPP Ga Buhari: Ka Sanya Dokar Ta Baci A Jihohin Arewa 5

Haka kuma ya zama damuwa ga zaman ‘ya’yanmu a gida wanda ba karamin matsala zai haifar ga yaranmu da mu kan mu iyaye.

Bisa ga hakan muna kira ga gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, ya sa baki domin kawo karshen yajin aikin malaman jami’o’in kasa nan .

Da yake jawabi shugaban NLC a jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhassan ya bayyana cewa “Shugabanni kwadagon sun fito kan tituna domin gudanar da zanga-zangar domin daliban da abin ya fi shafa su ne ‘ya’yan talakawa da ke makarantun gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

“ASUU ta shiga yajin aikin watanni biyar da suka gabata, kuma mafi yawan wadanda abin ya shafa ‘ya’yan talakawa ne, abin da muke yi a yau ba wai don kawo karshen yajin aikin ba ne, sai dai fafutukar ganin an samar da ingantaccen ilimi, kuma mafi kyawun ababen more rayuwa a cikin jami’o’i, inji shugaban.

Ya kara da cewa, NLC za ta ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana har sai an magance matsalar ta yadda ya kamata, inda ya jaddada cewa, ma’aikatan ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen shiga cikin kulle-kulle baki daya.

A nasa jawabin, shugaban ASUU na jihar Kebbi, Kwamared Yayale Ibrahim Danjuma,  ya ce “yajin aikin ya zama dole domin kara matsawa gwamnati lamba don ganin ta cika alkawarin da ta dauka.”

Yaa jaddada cewa, jami’o’in na da karancin kayan aikin koyar da dalibai, alhalin albashin malamai ba ya isarsu.

Hakazalika, shugaban kungiyar dalibai a jihar, Muhammed Muhaed Manjo, ya kuma bayyana cewa ilimi hakki ne na dukkan ‘ya’yan Nijeriya, ba gata ba ne, ya jaddada cewa, sun gaji da zama a gidajensu, ya kuma yaba wa ASUU, NLC da suka yi hadin gwiwa don gudanar da zanga-zangar lumana.

 

A sakon shugaban kungiyar NLC ta kasa, wanda ya shugaban kungiyar na jihar Kebbi ya wakilta , Kwamared Alhassa, a yayin gabatar da takardar zanga-zangar ta su ga Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, ya yaba wa gwamnan bisa kasancewa cikin gwamnoni biyar da suka biya ‘yan fansho garatuti da biyan albashin ma’aikata a kai a kai da kuma jajircewa wurin jin dadin al’umma a Jihar kebbi.

 

Ya bayyana cewa, sun je gidan gwamnati ne domin gabatar masa da wasikar zanga-zangar su domin ya shiga cikin maganar yajin aikin ASUU, ya jaddada cewa, a matsayinsa na shugaban kungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC da ya sa baki don kawo karshen yajin aikin da aka dade ana yi a jami’o’in kasa mu Nijeriya.

A nasa martanin, Glgwamna Abubakar Atiku Bagudu, wanda ya bayyana yajin aikin a matsayin abin damuwa, ya kuma bukaci kungiyoyin kwadago a jihar da su fito da hanyoyin da za a bi domin kawo karshen yajin aikin da kuma yadda za a samar da kudade a fannin ilimi a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Next Post
Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.