ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: NLC, ASUU da Sauran Kungiyoyi Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana A Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
Zanga-zanga

Kungiyar Kwadago Ta Kasa reshen Jihar Kebbi (NLC), tare da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da sauran kungiyoyi sun gudanar da zanga-zangar lumana a manyan titunan birnin Kebbi, a jihar Kebbi kan goyon bayan yajin aikin da ASUU ke yi.

Karkashin jagorancin shugaban kungiyar NLC reshen jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhasaan, masu zanga-zangar dauke da rubuce-rubuce daban-daban, kamar “kawo karshen yajin aikin ASUU yanzu, rufe jami’o’i yana da illa ga tattalin arziki, siyasa, likitanci, al’umma da shari’a.

  • Zaben Fidda-Gwanin PDP: Kotu Ta Fara Sauraren Karar Dan Majalisar Argungu/Augie a Kebbi
  • NNPP Ga Buhari: Ka Sanya Dokar Ta Baci A Jihohin Arewa 5

Haka kuma ya zama damuwa ga zaman ‘ya’yanmu a gida wanda ba karamin matsala zai haifar ga yaranmu da mu kan mu iyaye.

ADVERTISEMENT

Bisa ga hakan muna kira ga gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, ya sa baki domin kawo karshen yajin aikin malaman jami’o’in kasa nan .

Da yake jawabi shugaban NLC a jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhassan ya bayyana cewa “Shugabanni kwadagon sun fito kan tituna domin gudanar da zanga-zangar domin daliban da abin ya fi shafa su ne ‘ya’yan talakawa da ke makarantun gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

“ASUU ta shiga yajin aikin watanni biyar da suka gabata, kuma mafi yawan wadanda abin ya shafa ‘ya’yan talakawa ne, abin da muke yi a yau ba wai don kawo karshen yajin aikin ba ne, sai dai fafutukar ganin an samar da ingantaccen ilimi, kuma mafi kyawun ababen more rayuwa a cikin jami’o’i, inji shugaban.

Ya kara da cewa, NLC za ta ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana har sai an magance matsalar ta yadda ya kamata, inda ya jaddada cewa, ma’aikatan ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen shiga cikin kulle-kulle baki daya.

A nasa jawabin, shugaban ASUU na jihar Kebbi, Kwamared Yayale Ibrahim Danjuma,  ya ce “yajin aikin ya zama dole domin kara matsawa gwamnati lamba don ganin ta cika alkawarin da ta dauka.”

Yaa jaddada cewa, jami’o’in na da karancin kayan aikin koyar da dalibai, alhalin albashin malamai ba ya isarsu.

Hakazalika, shugaban kungiyar dalibai a jihar, Muhammed Muhaed Manjo, ya kuma bayyana cewa ilimi hakki ne na dukkan ‘ya’yan Nijeriya, ba gata ba ne, ya jaddada cewa, sun gaji da zama a gidajensu, ya kuma yaba wa ASUU, NLC da suka yi hadin gwiwa don gudanar da zanga-zangar lumana.

 

A sakon shugaban kungiyar NLC ta kasa, wanda ya shugaban kungiyar na jihar Kebbi ya wakilta , Kwamared Alhassa, a yayin gabatar da takardar zanga-zangar ta su ga Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, ya yaba wa gwamnan bisa kasancewa cikin gwamnoni biyar da suka biya ‘yan fansho garatuti da biyan albashin ma’aikata a kai a kai da kuma jajircewa wurin jin dadin al’umma a Jihar kebbi.

 

Ya bayyana cewa, sun je gidan gwamnati ne domin gabatar masa da wasikar zanga-zangar su domin ya shiga cikin maganar yajin aikin ASUU, ya jaddada cewa, a matsayinsa na shugaban kungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC da ya sa baki don kawo karshen yajin aikin da aka dade ana yi a jami’o’in kasa mu Nijeriya.

A nasa martanin, Glgwamna Abubakar Atiku Bagudu, wanda ya bayyana yajin aikin a matsayin abin damuwa, ya kuma bukaci kungiyoyin kwadago a jihar da su fito da hanyoyin da za a bi domin kawo karshen yajin aikin da kuma yadda za a samar da kudade a fannin ilimi a Nijeriya.

Zanga-zanga
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.