• Leadership Hausa
Sunday, October 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: NLC, ASUU da Sauran Kungiyoyi Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Kananan Labarai
0
Yajin Aikin ASUU: NLC, ASUU da Sauran Kungiyoyi Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago Ta Kasa reshen Jihar Kebbi (NLC), tare da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da sauran kungiyoyi sun gudanar da zanga-zangar lumana a manyan titunan birnin Kebbi, a jihar Kebbi kan goyon bayan yajin aikin da ASUU ke yi.

Karkashin jagorancin shugaban kungiyar NLC reshen jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhasaan, masu zanga-zangar dauke da rubuce-rubuce daban-daban, kamar “kawo karshen yajin aikin ASUU yanzu, rufe jami’o’i yana da illa ga tattalin arziki, siyasa, likitanci, al’umma da shari’a.

  • Zaben Fidda-Gwanin PDP: Kotu Ta Fara Sauraren Karar Dan Majalisar Argungu/Augie a Kebbi
  • NNPP Ga Buhari: Ka Sanya Dokar Ta Baci A Jihohin Arewa 5

Haka kuma ya zama damuwa ga zaman ‘ya’yanmu a gida wanda ba karamin matsala zai haifar ga yaranmu da mu kan mu iyaye.

Bisa ga hakan muna kira ga gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, ya sa baki domin kawo karshen yajin aikin malaman jami’o’in kasa nan .

Da yake jawabi shugaban NLC a jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhassan ya bayyana cewa “Shugabanni kwadagon sun fito kan tituna domin gudanar da zanga-zangar domin daliban da abin ya fi shafa su ne ‘ya’yan talakawa da ke makarantun gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 

NIS Reshen Ribas Za Ta Yi Kawance Da Gwamnatin Jihar Kan Zuba Jari Da Tsaron Gida

“ASUU ta shiga yajin aikin watanni biyar da suka gabata, kuma mafi yawan wadanda abin ya shafa ‘ya’yan talakawa ne, abin da muke yi a yau ba wai don kawo karshen yajin aikin ba ne, sai dai fafutukar ganin an samar da ingantaccen ilimi, kuma mafi kyawun ababen more rayuwa a cikin jami’o’i, inji shugaban.

Ya kara da cewa, NLC za ta ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana har sai an magance matsalar ta yadda ya kamata, inda ya jaddada cewa, ma’aikatan ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen shiga cikin kulle-kulle baki daya.

A nasa jawabin, shugaban ASUU na jihar Kebbi, Kwamared Yayale Ibrahim Danjuma,  ya ce “yajin aikin ya zama dole domin kara matsawa gwamnati lamba don ganin ta cika alkawarin da ta dauka.”

Yaa jaddada cewa, jami’o’in na da karancin kayan aikin koyar da dalibai, alhalin albashin malamai ba ya isarsu.

Hakazalika, shugaban kungiyar dalibai a jihar, Muhammed Muhaed Manjo, ya kuma bayyana cewa ilimi hakki ne na dukkan ‘ya’yan Nijeriya, ba gata ba ne, ya jaddada cewa, sun gaji da zama a gidajensu, ya kuma yaba wa ASUU, NLC da suka yi hadin gwiwa don gudanar da zanga-zangar lumana.

 

A sakon shugaban kungiyar NLC ta kasa, wanda ya shugaban kungiyar na jihar Kebbi ya wakilta , Kwamared Alhassa, a yayin gabatar da takardar zanga-zangar ta su ga Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, ya yaba wa gwamnan bisa kasancewa cikin gwamnoni biyar da suka biya ‘yan fansho garatuti da biyan albashin ma’aikata a kai a kai da kuma jajircewa wurin jin dadin al’umma a Jihar kebbi.

 

Ya bayyana cewa, sun je gidan gwamnati ne domin gabatar masa da wasikar zanga-zangar su domin ya shiga cikin maganar yajin aikin ASUU, ya jaddada cewa, a matsayinsa na shugaban kungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC da ya sa baki don kawo karshen yajin aikin da aka dade ana yi a jami’o’in kasa mu Nijeriya.

A nasa martanin, Glgwamna Abubakar Atiku Bagudu, wanda ya bayyana yajin aikin a matsayin abin damuwa, ya kuma bukaci kungiyoyin kwadago a jihar da su fito da hanyoyin da za a bi domin kawo karshen yajin aikin da kuma yadda za a samar da kudade a fannin ilimi a Nijeriya.

Tags: ASUUBirnin KebbiKebbiNlcZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Fidda-Gwanin PDP: Kotu Ta Fara Sauraren Karar Dan Majalisar Argungu/Augie a Kebbi

Next Post

Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

Related

Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 
Kananan Labarai

Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 

2 months ago
NIS Reshen Ribas Za Ta Yi Kawance Da Gwamnatin Jihar Kan Zuba Jari Da Tsaron Gida
Labarai

NIS Reshen Ribas Za Ta Yi Kawance Da Gwamnatin Jihar Kan Zuba Jari Da Tsaron Gida

2 months ago
Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama
Labarai

Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama

3 months ago
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Ilmantar Da Kamfanoni Kan Ƙa’idojin Aiki Da ‘Yan Ƙasashen Waje
Labarai

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Ilmantar Da Kamfanoni Kan Ƙa’idojin Aiki Da ‘Yan Ƙasashen Waje

3 months ago
Tashar Qausain TV Ta Karrama Pantami Da Lambar Yabo
Labarai

Tashar Qausain TV Ta Karrama Pantami Da Lambar Yabo

4 months ago
Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
Labarai

Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa

4 months ago
Next Post
Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.