• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

by Ibrahim Muhammad
10 months ago
in Labarai
0
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matakin Shugaban kasa, Bola Tinubu na kirkiro ma’aikatar bunkasa harkokin kiwo na ci gaba da janyo zafafan muhawara a tsakanin masu ruwa da tsaki.

Ko da yake, wani Lauya mai suna Madubuachi Idam, na kallon yunkurin na Tinubu a matsayin asara, domin akwai wasu ma’aikatun da ke da manufa irin aikin da wannan za ta yi, yayin da kuma kungiyar ci gaban matasan arewa (AYCF) da Afenifere da kuma Ohanaeze Ndigbo da suke da amannar wannan yunkurin abu ne mai kyau da zai iya kawo karshen matsalolin da ake samu tsakanin manoma da makiyaya.

  • Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar
  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

Tinubu ya kirkiri ma’aikatar ne da nufin kawo karshen rigingimun da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya da kuma ganin an inganta harkokin da suka shafi kiwo a fadin kasar nan.

Tun da farko dai, Tinubu ya kafa kwamiti bayan da ya amshi rahoton yadda za a bunkasa harkokin kiwon a kasar nan, wanda Abdullahi Ganduje ya jagoranta, kuma kwamitin ya gabatar da rahotonsa watanni goma da suka gabata da ya bayar da shawarar samar da ma’aikatar.

Sama da shekaru dai an jima ana samun rigingimu a tsakanin manoma da makiyaya wanda hakan ya janyo asarar rayuka da dukiyoyin da ba za su misaltu ba.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Jihohi kamar su Filato, Benuwai, Kaduna, Inugu, Imo, Delta, Oyo da wasu jihohin na daga cikin wuraren da aka fi samun wadannan matsalolin.

Sai dai Tinubu ya ce, ta hanyar samar da sabuwar ma’aikatar za a samu nasarar dakile wannan matsalar. Ya nuna cewa, shiga gonakai a yi barna da kuma toshe wa dabbobi hanyoyin kiwo duk za su samu sauki kuma za a samu rage asarar abinci da rage kaIfin matsaloli ta wannan ma’aikatar.

Sai dai Lauya Madubuachi Idam, ya soki lamarin da cewa an kirkiro ma’aikatar ne domin asarar dukiya a daidai lokacin da jama’an kasa ke kukan talauci da fatara.

Ya ce a maimakon hakan, kamatuwa ya yi a maida hankali kan ma’aikatar gona wanda za ta iya shawo kan lamuran da suka shafi kiwo ba wai sake kirkiro wata ma’aikata don bata kudin kasa ba.

Shi kuma a bangarensa, shugaban kungiyar ci gaban matasan arewa AYCF, Yerima Shettima, ya ce, kirkiro wannan ma’aikatar da Tinubu ya yi tabbas abun a jinjina masa ne kuma yanzu na da abun da zai iya bugan kirji ya nuna wa ‘yan Nijeriya cewa ya yi.

Shettima, ya yi fatan cewa ma’aikatar za ta samu nasarar kawo karshen rigingimun da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya, duk da ya misalta matakin a matsayin abun murna matuka.

Ya ce, “Mun yi murna sosai da muka ji labarin an samar da ma’aikatar kula da lamuran kiwo wannan na nuni da cewa gwamnatin nan na da abun da za ta nuna wa ‘yan Nijeriya cewa ta yi wajen ganin ta kawo karshen rikicin manoma da makiyaya.”

Ita ma kungiyar Fulanin ta MACBAN ta bakin daraktan yada labaranta reshen Jihar Kaduna, Ibrahim Bayero Zango, ya ce, tabbas ma’aikatar za ta share hawayen matsalolin da suke akwai kuma za ta kawo mafita ga rikicin manoma da makiyaya.

Zango ya sanya kafa ya shure ikirarin da ke cewa kirkirar ma’aikatar bata kudi ne kawai. Ya ce, ko da wasa ba asarar kudi za a yi ba, illa daura kasar zuwa turbar ci gaba.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan lamarin, darakta janar na kungiyar Ohanaeze, Okechukwu Isiguzoro, ya ce, ma’aikatar za ta shiga tsakanin rikicin manoma da makiyaya da kuma kawo mafita ta karshe, don haka ne suka jinjina wa samar da ma’aikatar.

Haka su ma kungiyar ci gaban al’ummar Yarbawa, Afenifere, ta ce dukkanin wani yunkurin da zai kawo karshen kai hare-haren tsakanin manoma da makiyaya abun yabawa ne kuma tabbas suna goyon bayan wannan yunkurin.

Kakakin kungiyar, Kwamarat Jare Ajayi, ya ce, ba su kallon matakin na Tinubu a kokarin fifita wani yanki ko wata kabila, illa wani mataki da zai kawo karshen matsalolin manoma da makiyaya. Ya nuna cewa ana samun matsalar rikicin manoma da makiyaya a kowani sassa na kasar nan, don haka ba wata kabila ko zallar yanki ne za su mori wannan ma’aikatar ba, illa dukkanin kasar ce za ta mora.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JegaLivestockSaniyaShanuTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Next Post

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

Related

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

1 hour ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

2 hours ago
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

4 hours ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

6 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

7 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

10 hours ago
Next Post
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.