ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

by Yusuf Shuaibu and Abubakar Sulaiman
2 years ago
Sarauta

A wani lamari na sauya sabon salo dangane da rikicin sarautar Kano, Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake maido da masarautu uku daga cikin hudu da ya rushe.

A rana daya Majalisar Dokokin Kano ta gabatar da kudirin samar da dokar kirkirar masauratun masu daraja ta biyu, aka yi mata karatun da ya kamata, aka zartar da dokar, sannan aka kai wa gwamna kuma ya rattaba mata hannu da yammacin ranar Talata.

Bayan gwamna ya rattaba wa dokar hannu, nan take kuma ya amince da nadin sabbin sarakuna masu daraja ta biyu da suka hada da masarautun Gaya, Rano da Karaye. Gwamnan ya nada Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin nadinsa shi ne Hakimin Rogo.

ADVERTISEMENT

Sai kuma Alhaji Muhammad Isa Umar, a matsayin Sarkin Rano, wanda kafin nadinsa shi ne Hakimin Bunkure, sannan kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya, a matsayin Sarkin Gaya, wanda shi ne tsohon Sarkin Gaya.

Wannan mataki na gwamnatin Jihar Kano ya zama wani sabon salo, domin a lokacin da ake tsaka da ce-ce-ku-ce a gaban kotuna daban-daban kan rikicin masarautun na Kano, an ji yadda wasu kotunan suka tabbatar da dakatar da Sarki Muhammadu Sanusi II da kotunan gwamnatin tarraya suka zartar tare da cin tarar gwamnatin Kano na naira miliyon 10. Haka itama wata kotu a Jihar Kano karkashin Mai Shari’a Amina ta tabbatar da haramta wa Sarki Aminu Ado da sauran sarakuna uku ayyana kansu a matsayin sarakuna.

LABARAI MASU NASABA

An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

Ana tsaka da wannan danbarwa ne sai kuma a ranar Talata da ta gabta, bayan dawowar majalisar dokokin Jihar Kano daga hutun sama da kwanaki 40, inda majalisar ta fara da wani kudiri da aka bukaci samar da dokar kirkirar masauratu masu daraja ta biyu, aka kuma amince tare da mika kunshin dokar, inda gwamnan ya rattaba mata hannu a lokaci guda kuma ya amince tare da nada sabbin sarakuna uku masu daraja ta biyu wadda a wannan rana aka mika masu takardun kama aiki

Wannan sabon mataki na gwamnatin Kano kan sarkakkiyar da ta dabaibaye masarautun Kano na nuni da cewa ga dukkan alamu sarakuna biyu uwa daya uba daya, Alhaji Aminu Ado Bayero da dan’uwansa, Alhaji Nasiru Ado Bayero na alamta cewar an tsame su daga cikin jerin sarakunan da ake magana akansu, musamman Masarautar Bichi wadda babu ita baki daya daga cikin sabuwar dokar.

Shi dai tsohon sarkin Gaya mai daraja ta daya, wanda yanzu kuma aka sake mayar da shi a matsayin sarkin na Gaya, amma a wannan karon mai daraja ta biyu, Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya rabauta da sake darewa kan karagar sarautar ta Gaya, sakamakon matakin da ya dauka tun a lokacin da Gwamnatin Abba ta sanar da sauke su, inda shi kadai ne wanda ya fito fili ya karbi wancan kaddarar, kila hakan tasa gwamna ya sake aminta da nadisa a matsayin sabon Sarkin Gaya a wani salo na saka masa bisa karbar hukumcin da gwamnati ta yanke a kansu tun da farko.

Sai dai kuma wadannan sabbin sarakuna masu daraja ta biyu an sare masu fika-fikai, domin sarkin Gaya na da iko ne kawai da kananan hukumomi uku, wanda suka hada da Gaya, Ajingi da Albasu, shi kuma Sarkin Rano na da kananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure, yayin da sarkin Karaye ke da iko da kananan hukumomin Karaye da Rogo, shi kuma Sarki Muhammadu Sanusi II sarki mai daraja ta daya kamar yadda sabuwar sokar ta nuna yana da kananan hukumomi 36 da suke karkashin ikonsa.

Sarauta
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Sarauta
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
Masarautu

An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano

August 21, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura
Masarautu

Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura

January 3, 2026
Next Post
GORON JUMA’A 19/07/2024

GORON JUMA'A 19/07/2024

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.