• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

by Yusuf Shuaibu and Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Masarautu
0
Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani lamari na sauya sabon salo dangane da rikicin sarautar Kano, Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake maido da masarautu uku daga cikin hudu da ya rushe.

A rana daya Majalisar Dokokin Kano ta gabatar da kudirin samar da dokar kirkirar masauratun masu daraja ta biyu, aka yi mata karatun da ya kamata, aka zartar da dokar, sannan aka kai wa gwamna kuma ya rattaba mata hannu da yammacin ranar Talata.

Bayan gwamna ya rattaba wa dokar hannu, nan take kuma ya amince da nadin sabbin sarakuna masu daraja ta biyu da suka hada da masarautun Gaya, Rano da Karaye. Gwamnan ya nada Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin nadinsa shi ne Hakimin Rogo.

Sai kuma Alhaji Muhammad Isa Umar, a matsayin Sarkin Rano, wanda kafin nadinsa shi ne Hakimin Bunkure, sannan kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya, a matsayin Sarkin Gaya, wanda shi ne tsohon Sarkin Gaya.

Wannan mataki na gwamnatin Jihar Kano ya zama wani sabon salo, domin a lokacin da ake tsaka da ce-ce-ku-ce a gaban kotuna daban-daban kan rikicin masarautun na Kano, an ji yadda wasu kotunan suka tabbatar da dakatar da Sarki Muhammadu Sanusi II da kotunan gwamnatin tarraya suka zartar tare da cin tarar gwamnatin Kano na naira miliyon 10. Haka itama wata kotu a Jihar Kano karkashin Mai Shari’a Amina ta tabbatar da haramta wa Sarki Aminu Ado da sauran sarakuna uku ayyana kansu a matsayin sarakuna.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin ÆŠaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan NaÉ—a Ma’ajin Hausawan Turai

Ana tsaka da wannan danbarwa ne sai kuma a ranar Talata da ta gabta, bayan dawowar majalisar dokokin Jihar Kano daga hutun sama da kwanaki 40, inda majalisar ta fara da wani kudiri da aka bukaci samar da dokar kirkirar masauratu masu daraja ta biyu, aka kuma amince tare da mika kunshin dokar, inda gwamnan ya rattaba mata hannu a lokaci guda kuma ya amince tare da nada sabbin sarakuna uku masu daraja ta biyu wadda a wannan rana aka mika masu takardun kama aiki

Wannan sabon mataki na gwamnatin Kano kan sarkakkiyar da ta dabaibaye masarautun Kano na nuni da cewa ga dukkan alamu sarakuna biyu uwa daya uba daya, Alhaji Aminu Ado Bayero da dan’uwansa, Alhaji Nasiru Ado Bayero na alamta cewar an tsame su daga cikin jerin sarakunan da ake magana akansu, musamman Masarautar Bichi wadda babu ita baki daya daga cikin sabuwar dokar.

Shi dai tsohon sarkin Gaya mai daraja ta daya, wanda yanzu kuma aka sake mayar da shi a matsayin sarkin na Gaya, amma a wannan karon mai daraja ta biyu, Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya rabauta da sake darewa kan karagar sarautar ta Gaya, sakamakon matakin da ya dauka tun a lokacin da Gwamnatin Abba ta sanar da sauke su, inda shi kadai ne wanda ya fito fili ya karbi wancan kaddarar, kila hakan tasa gwamna ya sake aminta da nadisa a matsayin sabon Sarkin Gaya a wani salo na saka masa bisa karbar hukumcin da gwamnati ta yanke a kansu tun da farko.

Sai dai kuma wadannan sabbin sarakuna masu daraja ta biyu an sare masu fika-fikai, domin sarkin Gaya na da iko ne kawai da kananan hukumomi uku, wanda suka hada da Gaya, Ajingi da Albasu, shi kuma Sarkin Rano na da kananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure, yayin da sarkin Karaye ke da iko da kananan hukumomin Karaye da Rogo, shi kuma Sarki Muhammadu Sanusi II sarki mai daraja ta daya kamar yadda sabuwar sokar ta nuna yana da kananan hukumomi 36 da suke karkashin ikonsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbakanoMasarauta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Darasi Daga Suratun Najmi (3): Ayoyin Allah Da Annabi (SAW) Ya Gani

Next Post

GORON JUMA’A 19/07/2024

Related

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

6 months ago
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin ÆŠaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan NaÉ—a Ma’ajin Hausawan Turai

11 months ago
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

12 months ago
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)
Masarautu

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

12 months ago
Tinubu Zai Halarci  Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa
Addini

Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

1 year ago
A Tsarin Mulki, Sarkin Musulmi Ba Shi Da Ikon NaÉ—a Wani – Gwamnatin Sokoto
Manyan Labarai

A Tsarin Mulki, Sarkin Musulmi Ba Shi Da Ikon NaÉ—a Wani – Gwamnatin Sokoto

1 year ago
Next Post
GORON JUMA’A 19/07/2024

GORON JUMA'A 19/07/2024

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.