• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

by Ibrahim Muhammad
12 months ago
in Labarai
0
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matakin Shugaban kasa, Bola Tinubu na kirkiro ma’aikatar bunkasa harkokin kiwo na ci gaba da janyo zafafan muhawara a tsakanin masu ruwa da tsaki.

Ko da yake, wani Lauya mai suna Madubuachi Idam, na kallon yunkurin na Tinubu a matsayin asara, domin akwai wasu ma’aikatun da ke da manufa irin aikin da wannan za ta yi, yayin da kuma kungiyar ci gaban matasan arewa (AYCF) da Afenifere da kuma Ohanaeze Ndigbo da suke da amannar wannan yunkurin abu ne mai kyau da zai iya kawo karshen matsalolin da ake samu tsakanin manoma da makiyaya.

  • Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar
  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

Tinubu ya kirkiri ma’aikatar ne da nufin kawo karshen rigingimun da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya da kuma ganin an inganta harkokin da suka shafi kiwo a fadin kasar nan.

Tun da farko dai, Tinubu ya kafa kwamiti bayan da ya amshi rahoton yadda za a bunkasa harkokin kiwon a kasar nan, wanda Abdullahi Ganduje ya jagoranta, kuma kwamitin ya gabatar da rahotonsa watanni goma da suka gabata da ya bayar da shawarar samar da ma’aikatar.

Sama da shekaru dai an jima ana samun rigingimu a tsakanin manoma da makiyaya wanda hakan ya janyo asarar rayuka da dukiyoyin da ba za su misaltu ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Jihohi kamar su Filato, Benuwai, Kaduna, Inugu, Imo, Delta, Oyo da wasu jihohin na daga cikin wuraren da aka fi samun wadannan matsalolin.

Sai dai Tinubu ya ce, ta hanyar samar da sabuwar ma’aikatar za a samu nasarar dakile wannan matsalar. Ya nuna cewa, shiga gonakai a yi barna da kuma toshe wa dabbobi hanyoyin kiwo duk za su samu sauki kuma za a samu rage asarar abinci da rage kaIfin matsaloli ta wannan ma’aikatar.

Sai dai Lauya Madubuachi Idam, ya soki lamarin da cewa an kirkiro ma’aikatar ne domin asarar dukiya a daidai lokacin da jama’an kasa ke kukan talauci da fatara.

Ya ce a maimakon hakan, kamatuwa ya yi a maida hankali kan ma’aikatar gona wanda za ta iya shawo kan lamuran da suka shafi kiwo ba wai sake kirkiro wata ma’aikata don bata kudin kasa ba.

Shi kuma a bangarensa, shugaban kungiyar ci gaban matasan arewa AYCF, Yerima Shettima, ya ce, kirkiro wannan ma’aikatar da Tinubu ya yi tabbas abun a jinjina masa ne kuma yanzu na da abun da zai iya bugan kirji ya nuna wa ‘yan Nijeriya cewa ya yi.

Shettima, ya yi fatan cewa ma’aikatar za ta samu nasarar kawo karshen rigingimun da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya, duk da ya misalta matakin a matsayin abun murna matuka.

Ya ce, “Mun yi murna sosai da muka ji labarin an samar da ma’aikatar kula da lamuran kiwo wannan na nuni da cewa gwamnatin nan na da abun da za ta nuna wa ‘yan Nijeriya cewa ta yi wajen ganin ta kawo karshen rikicin manoma da makiyaya.”

Ita ma kungiyar Fulanin ta MACBAN ta bakin daraktan yada labaranta reshen Jihar Kaduna, Ibrahim Bayero Zango, ya ce, tabbas ma’aikatar za ta share hawayen matsalolin da suke akwai kuma za ta kawo mafita ga rikicin manoma da makiyaya.

Zango ya sanya kafa ya shure ikirarin da ke cewa kirkirar ma’aikatar bata kudi ne kawai. Ya ce, ko da wasa ba asarar kudi za a yi ba, illa daura kasar zuwa turbar ci gaba.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan lamarin, darakta janar na kungiyar Ohanaeze, Okechukwu Isiguzoro, ya ce, ma’aikatar za ta shiga tsakanin rikicin manoma da makiyaya da kuma kawo mafita ta karshe, don haka ne suka jinjina wa samar da ma’aikatar.

Haka su ma kungiyar ci gaban al’ummar Yarbawa, Afenifere, ta ce dukkanin wani yunkurin da zai kawo karshen kai hare-haren tsakanin manoma da makiyaya abun yabawa ne kuma tabbas suna goyon bayan wannan yunkurin.

Kakakin kungiyar, Kwamarat Jare Ajayi, ya ce, ba su kallon matakin na Tinubu a kokarin fifita wani yanki ko wata kabila, illa wani mataki da zai kawo karshen matsalolin manoma da makiyaya. Ya nuna cewa ana samun matsalar rikicin manoma da makiyaya a kowani sassa na kasar nan, don haka ba wata kabila ko zallar yanki ne za su mori wannan ma’aikatar ba, illa dukkanin kasar ce za ta mora.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JegaLivestockSaniyaShanuTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Next Post

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

Related

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

3 hours ago
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

14 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

16 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

18 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

20 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

22 hours ago
Next Post
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

LABARAI MASU NASABA

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.