ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Gusau

Gusau ita da wasu wuraren da suke makwabtaka da ita an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa sun kasance ne a cikin birnin na masarautar.A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambo da hedikwatarta take a Gusau tana da wasu garuruwa da suke har ila yau karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da Gusau, kamar sauran sassan na daular Usumaniyya.

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki bayan da akwai wadanda suke taimakawa ita Gusau din wajen tafiyar mulki, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa shi garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayen su suke  haka,Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Sune suke wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni,da kuma Sarkin katsinan Gusau (Emir Of Gusau).Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarki.Gusau kamar sauran sassan da suke karkashi daular Usumaniyya suna aikawa da kason fadar Sarkin musulmi na irin kudaden da ta samu.

  • Rikicin Masarautar Kano: Tinubu Da Sanusi II Suna Da Alaka Mai Karfi – Fadar Shugaban Kasa
  • Har Yanzu Tukunyar Rikicin Masarautar Kano Na Tafarfasa

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’oin cigaba na garin Gusau da kungiyoyin da suke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa ma kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna, da wasu harkoki, manyan kamfanoni duk an kawo ma shi birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasa ta cigaban zamani.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da haka wasu tsare- tsaren mulkin mallaka da aka kawo sune suka sauya salo na mulkin.Idan ba haka b agarin na Gusau bai kai a rika  ba shi girma da daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanen lokaci lamurra sai suka canza.Lokacin mulkn mallaka na turawa ne aka fa amsar harajin dabbobi a shekarar 1907 da ake kira da suna  (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne sana’ar noma ta kasance babbar abar da take bunkasa tattalin arziki na garin Gusau,abin kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma.Sana’ar noma ta zama ba tad ana biyu idan ana maganar tattalin arziki ne wadda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona a ci da kuma sayarwa

LABARAI MASU NASABA

An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806- 1827

Wadannan Sarakunan shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida1916-1917

Sai dai kuma daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan da ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba Sarkin Katsinan Gusau 1984- 2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.

Gusau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
Masarautu

An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano

August 21, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura
Masarautu

Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura

January 3, 2026
Next Post
Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara – Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara - Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Gusau

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gusau

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.