• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya yi Allah-wadai da ikirarin da ake yi na cewa, “Shugaba Tinubu na adawa da Arewa”, inda ya ce, karya ne, kuma ikirarin sam bai dace ba.

Ya bayyana hakan ne a wata ziyarar ban girma da sabbin shugabannin kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) suka kai a gidan gwamnati Kaduna, inda ya bayyana ikirarin a matsayin makircin wasu kwararrun ‘yan siyasa.

  • Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 
  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro Da Talauci A Arewa

A cewarsa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ba gwamnatocin jihohin Arewa goyon baya irin wanda ba a saba gani ba don magance dimbin kalubalen da suke fuskanta.

 

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa, dole ne masu ruwa da tsaki a Arewa su fada wa kansu gaskiya sannan su hada kai don samar da dabarun bai daya don magance kalubalen ci gaba, tare da tunkarar masu aikata laifuka da ke haddasa wa al’umma kuncin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Uba sani

Ya yi nuni da cewa, sabon kwamitin zartaswa na ACF ya zo a daidai lokacin da ake fama da manyan kalubale da ke fuskantar yankin Arewa.

 

“Muna fuskantar matsaloli masu wuya game da sha’anin tsaro da ke hana ci gaba. Masu aikata laifuka sun mamaye al’ummomin Arewa suna wargaza ci gaban da ta samu ta fuskoki da dama. Rashin ci gaban mu (Yankin Arewa) yana da ban tsoro kuma yana buƙatar kulawa cikin gaggawa ”

Uba sani

Ya ci gaba da bayyana cewa, a bayyane yake cewa, Arewacin Nijeriya na fuskantar barazanar wanzuwa kuma lokaci ya yi da kowa ya kamata ya tashi tsaye wajen kawar da yankin daga durkushewa.

 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa, ya kamata ‘yan Arewacin Nijeriya su daina zargin wane ne ko wacce ce matsalar Arewa, kamata ya yi a nemo ta yadda asalin matsalar ta faro.

 

“Mun kasa yi wa kanmu wasu muhimman tambayoyi. Ta ina matsalar ta faro a Arewa? Su wane ne masu hannu a cikin rashin ci gaban Arewa? Me muka yi a daidaiku da jama’a don nemo hanyoyin magance kalubalen da Arewa ke fuskanta?

 

A cewarsa, kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF na da babban rawar da za ta taka wajen samar da matsayar da ake bukata domin ganin an shawo kan kalubale iri-iri da ke fuskantar Arewacin Nijeriya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abubakar Sani BelloACFKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yarjejeniyar Beijing: Mabudin Zaman Lafiya A Zirin Gaza

Next Post

Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 hour ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

1 hour ago
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

4 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

7 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

8 hours ago
Next Post
Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

LABARAI MASU NASABA

Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.