ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Nijeriya

Kamfanin Man Fetur na Ƙasa na Nijeriya (NNPCL) ya bayyana cewa ƙasar na burin samun jarin Dala biliyan 60 cikin shekaru biyar zuwa bakwai masu zuwa domin faɗaɗa fannin iskar gas.

Babban Jami’in Gudanarwa na NNPCL, Mista Bayo Ojulari, ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga masu sauraro daga ƙasashe 150 a wajen buɗe taron Gastech Exhibition da Conference da aka gudanar a Milan, Ƙasar Italiya. Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na neman wannan jarin ne don ƙarfafa masana’antu da kuma tabbatar da matsayi mai ƙarfi na Nijeriya a kasuwar makamashi ta duniya.

  • Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

A cewarsa, jarin da aka tsara zai mayar da hankali ne wajen haɓaka samar da iskar gas na asali a Nijeriya zuwa biliyan 12 na cubic feet a kowace rana da kuma faɗaɗa ƙarfin masana’antar tace mai domin biyan ƙaruwar buƙatar makamashi da ake samu ta duniya.

ADVERTISEMENT

“Muna neman aƙalla jarin Dala biliyan 60 cikin shekaru biyar zuwa bakwai masu zuwa, wanda ake buƙata ga masana’antar mai da iskar gas ɗinmu. Wannan ya taƙaita ne a ƙaramin ɓangare kawai. Mun na neman masu zuba jari domin haɓaka samar da kayayyaki,” in ji shi.

Ojulari ya bayyana cewa Dokar Masana’antar Mai da Gas (Petroleum Industry Act – PIA), wadda aka sanya wa hannu a 2021, ta sauya NNPC zuwa kamfani mai iyaka (limited liability company), wanda ya bai wa kamfanin damar samun kuɗaɗen kai tsaye da kuma kafa haɗin gwiwa na duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ya ce a halin yanzu kamfanin na samar da kimanin ganga miliyan 1.6 na mai a kowace rana (bpd) tare da burin haɓaka samarwa zuwa miliyan 2 bpd nan da shekara ta 2027 da miliyan 3 bpd nan da 2030. Ya haskaka ayyukan da ake gudanarwa a halin yanzu, ciki har da bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), faɗaɗa West African Gas Pipeline zuwa Morocco da Turai, da kuma haɓaka aikin Nigeria LNG.

A cewarsa, Nijeriya tana samar da kashi 60 cikin ɗari na LNG ga Portugal da Sipaniya, kuma a halin yanzu tana kan Train 6, tana gina Train 7 wanda za a kammala a shekara ta 2026, tare da shirin gina Trains 8 da 9. “Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashen da ke da mafi kyawun harkokin LNG a duniya. Muna son amfani da babbar buƙatar makamashi a yanzu, wadda ake sa ran za ta ƙaru sosai nan gaba,” in ji shi.

Game da makamashi mai tsafta, Ojulari ya ce gwamnati na ƙarfafa amfani da LPG kuma ta ƙaddamar da shirin rarraba silinda miliyan 2 a faɗin ƙasar, yayin da ake kuma aiwatar da shirin canjin motoci da na’urori zuwa Compressed Natural Gas (CNG).

Game da rawar Nijeriya a harkar tsaron makamashi na duniya, ya ƙara da cewa sauye-sauyen siyasa a duniya, kamar yakin Rasha da Ukraine, sun hanzarta aiwatar da ayyukan bututun iskar gas na yanki domin ƙarfafa tsaron makamashi. Shugaban NNPCL ya ce Nijeriya na da filayen mai da iskar gas sama da 200 da ba a haɓaka ba, inda ya bayyana su a matsayin damammaki masu kyau ga masu zuba jari na ƙasashen waje.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

MASU ALAKA

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja
Manyan Labarai

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Next Post
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

LABARAI MASU NASABA

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.