ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Nijeriya

Kamfanin Man Fetur na Ƙasa na Nijeriya (NNPCL) ya bayyana cewa ƙasar na burin samun jarin Dala biliyan 60 cikin shekaru biyar zuwa bakwai masu zuwa domin faɗaɗa fannin iskar gas.

Babban Jami’in Gudanarwa na NNPCL, Mista Bayo Ojulari, ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga masu sauraro daga ƙasashe 150 a wajen buɗe taron Gastech Exhibition da Conference da aka gudanar a Milan, Ƙasar Italiya. Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na neman wannan jarin ne don ƙarfafa masana’antu da kuma tabbatar da matsayi mai ƙarfi na Nijeriya a kasuwar makamashi ta duniya.

  • Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

A cewarsa, jarin da aka tsara zai mayar da hankali ne wajen haɓaka samar da iskar gas na asali a Nijeriya zuwa biliyan 12 na cubic feet a kowace rana da kuma faɗaɗa ƙarfin masana’antar tace mai domin biyan ƙaruwar buƙatar makamashi da ake samu ta duniya.

ADVERTISEMENT

“Muna neman aƙalla jarin Dala biliyan 60 cikin shekaru biyar zuwa bakwai masu zuwa, wanda ake buƙata ga masana’antar mai da iskar gas ɗinmu. Wannan ya taƙaita ne a ƙaramin ɓangare kawai. Mun na neman masu zuba jari domin haɓaka samar da kayayyaki,” in ji shi.

Ojulari ya bayyana cewa Dokar Masana’antar Mai da Gas (Petroleum Industry Act – PIA), wadda aka sanya wa hannu a 2021, ta sauya NNPC zuwa kamfani mai iyaka (limited liability company), wanda ya bai wa kamfanin damar samun kuɗaɗen kai tsaye da kuma kafa haɗin gwiwa na duniya.

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Ya ce a halin yanzu kamfanin na samar da kimanin ganga miliyan 1.6 na mai a kowace rana (bpd) tare da burin haɓaka samarwa zuwa miliyan 2 bpd nan da shekara ta 2027 da miliyan 3 bpd nan da 2030. Ya haskaka ayyukan da ake gudanarwa a halin yanzu, ciki har da bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), faɗaɗa West African Gas Pipeline zuwa Morocco da Turai, da kuma haɓaka aikin Nigeria LNG.

A cewarsa, Nijeriya tana samar da kashi 60 cikin ɗari na LNG ga Portugal da Sipaniya, kuma a halin yanzu tana kan Train 6, tana gina Train 7 wanda za a kammala a shekara ta 2026, tare da shirin gina Trains 8 da 9. “Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashen da ke da mafi kyawun harkokin LNG a duniya. Muna son amfani da babbar buƙatar makamashi a yanzu, wadda ake sa ran za ta ƙaru sosai nan gaba,” in ji shi.

Game da makamashi mai tsafta, Ojulari ya ce gwamnati na ƙarfafa amfani da LPG kuma ta ƙaddamar da shirin rarraba silinda miliyan 2 a faɗin ƙasar, yayin da ake kuma aiwatar da shirin canjin motoci da na’urori zuwa Compressed Natural Gas (CNG).

Game da rawar Nijeriya a harkar tsaron makamashi na duniya, ya ƙara da cewa sauye-sauyen siyasa a duniya, kamar yakin Rasha da Ukraine, sun hanzarta aiwatar da ayyukan bututun iskar gas na yanki domin ƙarfafa tsaron makamashi. Shugaban NNPCL ya ce Nijeriya na da filayen mai da iskar gas sama da 200 da ba a haɓaka ba, inda ya bayyana su a matsayin damammaki masu kyau ga masu zuba jari na ƙasashen waje.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

MASU ALAKA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.