• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Baro Shiri Tun Rani Game Da Shigo Da Abinci Ba Tare Da Biyan Haraji Ba

by Abubakar Abba
11 months ago
in Labarai
0
An Baro Shiri Tun Rani Game Da Shigo Da Abinci Ba Tare Da Biyan Haraji Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta amince da shigo da abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, har na tsawon kwanaki 150; ba tare da biyan ko sisin kwabo a matsayin haraji ba.

Har ila yau, kayan abincin da gwamnatin ta amince a shigo da su din sun hada da; Masara, Shinkafa, Alkama da sauran makamantansu, wanda ta ce; ta dauki wannan mataki ne, domin dakile hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin wannan kasa baki-daya, kamar yadda Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya shaida wa manema labarai a Abuja.

  • Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu
  • Gwamnatin Kano Ta Sayi Taki Tirela 180 Domin Bunkasa Noma A Jihar

Sai dai kuma, wakilinmu ya ji ta bakin wasu masu ruwa da tsaki wadanda kuma manoma ne a kan wannan batu, inda akasarinsu suka nuna cewa, gwamnatin ta riga ta baro shiri tun rani.

Haka zalika, daya daga cikinsu; Alhaji Adamu Makarfi, Shugaban Manoman Masara na Arewa Maso Yamma; a hirarsa da LEADERSHIP Hausa ya bayyana cewa, wannan mataki; ko kadan ba zai haifar wa da Nijeriya da mai Ido ba, domin kuwa kamata ya yi bayan an zabi Shugaba Tinubu a matsayin shugaban kasa; ya ayyana dokar ta baci a fannin aikin noma, musamman ta fuskar magance kalubalen rashin tsaro, duba da yadda ake kashe manoma a Arewacin wannan kasa babu ji babu gani. Haka zalika, kyautuwa ya yi a ce ya wanzar da kudurinsa na magance kalubalen rashin tsaron, ta yadda ‘yan kasa za su gani a kasa, ba kawai kuma sai a siyasantar da fannin ba; da sunan daukar matakin shigo da abinci ba tare da biyan haraji ba, domin duk kasar da aka ce babu abinci, ko shakka babu za ta kasance cikin babbar fitina da halin dardar.

Makarfi ya ci gaba da cewa, akasari tun kafin zuwan wannan gwamnati, ana sayar wa da manoma takin zamani ne a kurarren lokaci; sannan kuma da matukar tsada duba da yadda kusan a bana, aka sayar da takin zamanin a kan kusan farashin Naira 40,000 duk buhu guda, wanda hakan ke jawo musu dimbin asara, musamman ma kananan manoma.

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Kazalika, ya yi nuni da cewa; kamata ya yi a rika sayar musu da takin zamanin a kan lokaci, sannan kuma gwamnati ta sayar musu da shi cikin rahusa, wanda hakan zai ba su kwarin gwaiwar noma amfani mai yawa; wanda zai iya wadatar da wannan kasa.

Ita ma wata manomiya, Hajiya Aisha Abubakar a hirarta da wakilinmu ta bayyana cewa, matakin gwamnatin tarayyar ba zai wadatar wajen karya farashin abinci ba, domin kuwa Nijeriya na bukatar dimbin tantan na abinci; kafin a iya wadata kasar da abinci, musamman duba da karuwar yawan al’ummar kasar a halin yanzu.

Ta kara da cewa, rashin sama wa manoman ingantacce Irin noma, hakan na jawo musu tabka asara da kuma rashin mayar da hankali a bangaren gwamnati, musamman gwamnatin tarayya na samar da kayan aikin noma na zamani; wanda ko shakka babu ke yi wa fannin matukar illa tare da samar da koma baya.

Shi kuwa wani babban manomi, a bangare guda kuma tsohon shugaban kunkiyar masu kiwon kajin gidan gona, reshen Jihar Kaduna; Alhaji Musa Bala a zantawarsa da LEADERSHIP Hausa ya yi nuni da cewa, matakin gwamnatin tarayyar; tamkar riga Malam Masallaci ne, domin kuwa ko da an shigo da abincin,  akwai wasu baragurbin da za su saye baki-daya; su kuma rika sayar wa da al’umma, musamman talakawa a kan farashi mai matukar tsada.

Bala ya kara da cewa, kamata ya yi yadda Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci  a wannan fanni, sai kuma ya sa a dawo da tsari irin na da; wato na kafa hukumar kayyade farashin kayayyaki, musamman kayan abinci; amma wannan mataki na shigo da kayan abincin cikin wannan kasa, musamman domin magance hauhawar farashin kayan; ba zai taba yin wani tasiri ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciFood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Koko Zuwa Tan 500,000 A 2025

Next Post

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

18 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Abinci
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Abinci

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.