• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Baro Shiri Tun Rani Game Da Shigo Da Abinci Ba Tare Da Biyan Haraji Ba

by Abubakar Abba
1 year ago
in Labarai
0
An Baro Shiri Tun Rani Game Da Shigo Da Abinci Ba Tare Da Biyan Haraji Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta amince da shigo da abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, har na tsawon kwanaki 150; ba tare da biyan ko sisin kwabo a matsayin haraji ba.

Har ila yau, kayan abincin da gwamnatin ta amince a shigo da su din sun hada da; Masara, Shinkafa, Alkama da sauran makamantansu, wanda ta ce; ta dauki wannan mataki ne, domin dakile hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin wannan kasa baki-daya, kamar yadda Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya shaida wa manema labarai a Abuja.

  • Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu
  • Gwamnatin Kano Ta Sayi Taki Tirela 180 Domin Bunkasa Noma A Jihar

Sai dai kuma, wakilinmu ya ji ta bakin wasu masu ruwa da tsaki wadanda kuma manoma ne a kan wannan batu, inda akasarinsu suka nuna cewa, gwamnatin ta riga ta baro shiri tun rani.

Haka zalika, daya daga cikinsu; Alhaji Adamu Makarfi, Shugaban Manoman Masara na Arewa Maso Yamma; a hirarsa da LEADERSHIP Hausa ya bayyana cewa, wannan mataki; ko kadan ba zai haifar wa da Nijeriya da mai Ido ba, domin kuwa kamata ya yi bayan an zabi Shugaba Tinubu a matsayin shugaban kasa; ya ayyana dokar ta baci a fannin aikin noma, musamman ta fuskar magance kalubalen rashin tsaro, duba da yadda ake kashe manoma a Arewacin wannan kasa babu ji babu gani. Haka zalika, kyautuwa ya yi a ce ya wanzar da kudurinsa na magance kalubalen rashin tsaron, ta yadda ‘yan kasa za su gani a kasa, ba kawai kuma sai a siyasantar da fannin ba; da sunan daukar matakin shigo da abinci ba tare da biyan haraji ba, domin duk kasar da aka ce babu abinci, ko shakka babu za ta kasance cikin babbar fitina da halin dardar.

Makarfi ya ci gaba da cewa, akasari tun kafin zuwan wannan gwamnati, ana sayar wa da manoma takin zamani ne a kurarren lokaci; sannan kuma da matukar tsada duba da yadda kusan a bana, aka sayar da takin zamanin a kan kusan farashin Naira 40,000 duk buhu guda, wanda hakan ke jawo musu dimbin asara, musamman ma kananan manoma.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Kazalika, ya yi nuni da cewa; kamata ya yi a rika sayar musu da takin zamanin a kan lokaci, sannan kuma gwamnati ta sayar musu da shi cikin rahusa, wanda hakan zai ba su kwarin gwaiwar noma amfani mai yawa; wanda zai iya wadatar da wannan kasa.

Ita ma wata manomiya, Hajiya Aisha Abubakar a hirarta da wakilinmu ta bayyana cewa, matakin gwamnatin tarayyar ba zai wadatar wajen karya farashin abinci ba, domin kuwa Nijeriya na bukatar dimbin tantan na abinci; kafin a iya wadata kasar da abinci, musamman duba da karuwar yawan al’ummar kasar a halin yanzu.

Ta kara da cewa, rashin sama wa manoman ingantacce Irin noma, hakan na jawo musu tabka asara da kuma rashin mayar da hankali a bangaren gwamnati, musamman gwamnatin tarayya na samar da kayan aikin noma na zamani; wanda ko shakka babu ke yi wa fannin matukar illa tare da samar da koma baya.

Shi kuwa wani babban manomi, a bangare guda kuma tsohon shugaban kunkiyar masu kiwon kajin gidan gona, reshen Jihar Kaduna; Alhaji Musa Bala a zantawarsa da LEADERSHIP Hausa ya yi nuni da cewa, matakin gwamnatin tarayyar; tamkar riga Malam Masallaci ne, domin kuwa ko da an shigo da abincin,  akwai wasu baragurbin da za su saye baki-daya; su kuma rika sayar wa da al’umma, musamman talakawa a kan farashi mai matukar tsada.

Bala ya kara da cewa, kamata ya yi yadda Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci  a wannan fanni, sai kuma ya sa a dawo da tsari irin na da; wato na kafa hukumar kayyade farashin kayayyaki, musamman kayan abinci; amma wannan mataki na shigo da kayan abincin cikin wannan kasa, musamman domin magance hauhawar farashin kayan; ba zai taba yin wani tasiri ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciFood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Koko Zuwa Tan 500,000 A 2025

Next Post

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

Related

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

8 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

10 hours ago
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

10 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

10 hours ago
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
Labarai

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

11 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

11 hours ago
Next Post
Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

LABARAI MASU NASABA

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.