ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Baro Shiri Tun Rani Game Da Shigo Da Abinci Ba Tare Da Biyan Haraji Ba

by Abubakar Abba
2 years ago
Abinci

A kwanakin baya ne, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta amince da shigo da abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, har na tsawon kwanaki 150; ba tare da biyan ko sisin kwabo a matsayin haraji ba.

Har ila yau, kayan abincin da gwamnatin ta amince a shigo da su din sun hada da; Masara, Shinkafa, Alkama da sauran makamantansu, wanda ta ce; ta dauki wannan mataki ne, domin dakile hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin wannan kasa baki-daya, kamar yadda Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya shaida wa manema labarai a Abuja.

  • Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu
  • Gwamnatin Kano Ta Sayi Taki Tirela 180 Domin Bunkasa Noma A Jihar

Sai dai kuma, wakilinmu ya ji ta bakin wasu masu ruwa da tsaki wadanda kuma manoma ne a kan wannan batu, inda akasarinsu suka nuna cewa, gwamnatin ta riga ta baro shiri tun rani.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, daya daga cikinsu; Alhaji Adamu Makarfi, Shugaban Manoman Masara na Arewa Maso Yamma; a hirarsa da LEADERSHIP Hausa ya bayyana cewa, wannan mataki; ko kadan ba zai haifar wa da Nijeriya da mai Ido ba, domin kuwa kamata ya yi bayan an zabi Shugaba Tinubu a matsayin shugaban kasa; ya ayyana dokar ta baci a fannin aikin noma, musamman ta fuskar magance kalubalen rashin tsaro, duba da yadda ake kashe manoma a Arewacin wannan kasa babu ji babu gani. Haka zalika, kyautuwa ya yi a ce ya wanzar da kudurinsa na magance kalubalen rashin tsaron, ta yadda ‘yan kasa za su gani a kasa, ba kawai kuma sai a siyasantar da fannin ba; da sunan daukar matakin shigo da abinci ba tare da biyan haraji ba, domin duk kasar da aka ce babu abinci, ko shakka babu za ta kasance cikin babbar fitina da halin dardar.

Makarfi ya ci gaba da cewa, akasari tun kafin zuwan wannan gwamnati, ana sayar wa da manoma takin zamani ne a kurarren lokaci; sannan kuma da matukar tsada duba da yadda kusan a bana, aka sayar da takin zamanin a kan kusan farashin Naira 40,000 duk buhu guda, wanda hakan ke jawo musu dimbin asara, musamman ma kananan manoma.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kazalika, ya yi nuni da cewa; kamata ya yi a rika sayar musu da takin zamanin a kan lokaci, sannan kuma gwamnati ta sayar musu da shi cikin rahusa, wanda hakan zai ba su kwarin gwaiwar noma amfani mai yawa; wanda zai iya wadatar da wannan kasa.

Ita ma wata manomiya, Hajiya Aisha Abubakar a hirarta da wakilinmu ta bayyana cewa, matakin gwamnatin tarayyar ba zai wadatar wajen karya farashin abinci ba, domin kuwa Nijeriya na bukatar dimbin tantan na abinci; kafin a iya wadata kasar da abinci, musamman duba da karuwar yawan al’ummar kasar a halin yanzu.

Ta kara da cewa, rashin sama wa manoman ingantacce Irin noma, hakan na jawo musu tabka asara da kuma rashin mayar da hankali a bangaren gwamnati, musamman gwamnatin tarayya na samar da kayan aikin noma na zamani; wanda ko shakka babu ke yi wa fannin matukar illa tare da samar da koma baya.

Shi kuwa wani babban manomi, a bangare guda kuma tsohon shugaban kunkiyar masu kiwon kajin gidan gona, reshen Jihar Kaduna; Alhaji Musa Bala a zantawarsa da LEADERSHIP Hausa ya yi nuni da cewa, matakin gwamnatin tarayyar; tamkar riga Malam Masallaci ne, domin kuwa ko da an shigo da abincin,  akwai wasu baragurbin da za su saye baki-daya; su kuma rika sayar wa da al’umma, musamman talakawa a kan farashi mai matukar tsada.

Bala ya kara da cewa, kamata ya yi yadda Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci  a wannan fanni, sai kuma ya sa a dawo da tsari irin na da; wato na kafa hukumar kayyade farashin kayayyaki, musamman kayan abinci; amma wannan mataki na shigo da kayan abincin cikin wannan kasa, musamman domin magance hauhawar farashin kayan; ba zai taba yin wani tasiri ba.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.