ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu

by Bello Hamza
2 years ago
Amurka

A halin yanzu Nijeriya da kasar Amurka sun jaddada shirin kara karfafa harkokin kasuwanci da zuba jari a tsakaninsu.

 

Wannann ya biyo bayan taron koli nena kasashen da ya gudana a tsakanin Ministar Masa’anatu, Kasuwanci da Zuba Jari na Nijeriya, Dakta Doris Uzoka-Anite, da tawagar kasar Amurka a karkashin jagorancin mataimakin sakatare mai kula da harkokin ciniki da kasuwanci tsakanin kasashen waje, Mista Arun Benkataraman, a Abuja ranar Laraba.

ADVERTISEMENT
  • Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

Taron ya mayar da hankali ne wajen karfafawa tare da tabbatar da yarjejeniyar da ke tsakanin kasashen biyu da suka hada da shirin nan na (TIFA) da (AGOA) da (BNC) da kuma (CID) wadanda ke karfafa kasuwanci a tsakanin kasashen Afrika da duniya baki daya ba a manta da su ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Duka bangarorin sun karfafa bukatar fadada harkokin kasuwanci a tsakaninsu tare da kuma kirkiro da sabbin hanyoyin cimma bukatun kasashen nasu domin bunkasa tattalin arzikin juna.

 

Dakta Uzoka-Anite ta bayyana abubuwan da Amurka za ta amfana dasu a Nijeriya wadanda suka hada da kasancewar ta babbar kasuwar da babu irinta a nan kusa da kuma ma’adanai da Allah ya hore mana a sassan kasa, haka kuma muna da kwararru masu ilimi daban-daban da za a iya fitar dasu zuwa kasashen waje su amfanar da kasashe daban-daban,” in ji ta.

 

Ta kuma jinjina wa dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka. “Nijeriya da Amurka sun dade suna hulda da juna na tsawon shekaru, suna mutunta juna tare da amfanar juna a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji ta.

 

A nasa jawabin, Benkataraman ya sanar da goyon bayan Amurka ga shirin farfado da tattalin arzikn kasa da kuma irin kalubalen da kamfanonin Amurka da ke harkoki a Nijeriya ke fuskanta.

 

“Za mu yi aiki domin karfafa dangantakar da ke tsakanin mu domin samun ci gaba da bunkasar tattalin arziki ta yadda al’ummar kasashen biyu za su amfana,” in ji shi.

 

Tawagar ta kasa Amurka ta nuna sha’awarta ga sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu take yi, sun kuma yi alkawarin bayar da gudummawarsu wajen karfafa kasuwanci da zuba jari a Nijeriya a daidai wannan lokacin.

 

Duka bangarorin sun amince da ci gaba da tattaunawa akai akai tsakaninsu don tabbatar da dorewar yarjejeniyar da aka kulla. An kammala taron tare da alkawarin kara karfafa kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu.

Amurka
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
Tattalin Arziki

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Next Post
BUK

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.