• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa

by Bello Hamza
10 months ago
in Labarai
0
Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Fulani ta ‘Miyatti Allah Cattle Breeders Association of Niger (MACBAN)’ reshen jihar Katsina, ta nesanta kanta daga zanga-zangar da aka shiryawa gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu domin halin yunwa da wahala da ‘yan Nijeriya ke fama da shi.

Kungiyar ta ce wasu ne ke cusa wa matasan wannan ra’ayi su yi wa gwamnati bore, wanda ta ce zanga-zangar ka iya rikidewa ta koma tashin hankali.

  • Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika
  • Goron Juma’a

Kungiyar ta bayyana hakan ne ta hannun Abdullahi Ismail, Sakatare na kungiyar reshen jihar Katsina a wata ganawa da ya yi da manema labarai.

Ismail ya ce; “na zo nan domin mu yi kira ga matasa wadanda za a yi amfani da su domin cimma manufa; akan suna korafi da yunwa da tsanani na rayuwa dake damun al’umma. Bayan kuma wasu ne ke cusa musu wannan ra’ayin. Wanda a zahirin gaskiya abin ba nan ya dosa ba. Shiyasa muke kiran al’umma musamman matasanmu da ka da a yi amfani da su wajen yi ma gwamnati barna ko wajen kawo wani rudani a cikin kasa”, ya shawarce su.

Sannan ya ci gaba da cewa; “matasan na duba da irin kasashen Kenya da sauran kasashe da suke irin wannan zanga-zanga. Mutanen wadancan wuraren suna yi ne domin kasar su da ci gabanta. Amma mu a fahimtarmu wannan zanga-zangar da za a yi ba zanga-zanga ba ce ta ci gaban al’ummar Nijeriya, wasu ne suka kirkire shi domin cimma manufofinsu”, in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Kungiyar ta ci gaba da cewa; “a kan haka, shugaban kungiyar tabbatar da dimokuradiyya a Nijeriya, Honorabul Abdurrahman Buba Kwacham, ya tara wannan taro ya kira mutane masu ruwa da tsaki a kan shugabanci na matasa da abin da ya shafi arewacin Nijeriya da ma kasar baki daya a kan a gaya wa mutane muhimmancin rashin shiga cikin wannan zanga-zanga da za a yi”.

Kungiyar ta ce zanga-zangar ba na gaskiya bane, na cimma wadansu manufofi ne. “Ba ana yi bane domin wahalar da kasar ke ciki. Idan domin matsalolin da kasa ke ciki ne, akwai shirye-shirye da yawa da gwamnati ta yi, domin magance wadannan matsalolin”, ya labarta.

Ya nesanta kungiyar da cewa gwamnati ta siye su ne su kashe kwarin guiwar matasan, inda ya jaddada cewa; gwamnati ba ta siye su ba; sai dai ya yarda cewa akwai damuwa ta rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fama da shi; “amma gwamnati na kan kokarin ganin ta magance wannan matsalolin. Hakan yasa muke ganin bai kamata matasa su sanya kansu a cikin wannan zanga-zanga ba”, ya lurantar.

Kungiyar ta ce ‘yancin gashin kai da aka bai wa kananan hukumomin Nijeriya, a ganin su tabbas zai magance matsaloli na tsaro sannan za a samu sauki; “domin ba sai sun jira gwamnatin jiha ko na tarayya ta kawo dauki ba. Domin suna da komai a hannunsu wanda za su yi amfani da shi domin magance matsalar tsaro domin taimaka ma al’umma”, in ji shi.

Da yake tabbatar da irin wahalar rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fuskanta ya ce; tabbas akwai matsaloli wanda ya hassala ‘yan Nijeriya, amma akwai wadanda za su yi amfani da zanga-zangar wajen cimma manufofinsu, “akwai wadanda za su zo su bi masu yin abin don Allah, masu yi domin ci gaban kasar, su shiga cikinsu su rika balla shagunan mutane suna kawo rudani a cikin al’umma. Wanda daga karshe duk zai tafi da sunan wannan zanga-zangar da aka shirya a kan yunwa da tsananin rayuwa, bayan kuma a zahiri ba haka bane.

Ya karkare da cewa; “muna yin abu ne domin kyautata rayuwar matasa. Muna shugabantar matasa ne. Hakan ya sa mu ka ga ya kyautu mu kira matasan nan mu sanar da su cewa wannan abin da suke yi idan suka tafi da shi, akwai wadanda za su shigo bata gari su canza ma abin tsari da kuduri wanda suke kan shi”, in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FulaniKungiyaMACBANMatasaZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

Next Post

Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
Labarai

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

8 hours ago
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
Labarai

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

12 hours ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

13 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

13 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

14 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.