ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa

by Bello Hamza
1 year ago
MACBAN

Kungiyar Fulani ta ‘Miyatti Allah Cattle Breeders Association of Niger (MACBAN)’ reshen jihar Katsina, ta nesanta kanta daga zanga-zangar da aka shiryawa gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu domin halin yunwa da wahala da ‘yan Nijeriya ke fama da shi.

Kungiyar ta ce wasu ne ke cusa wa matasan wannan ra’ayi su yi wa gwamnati bore, wanda ta ce zanga-zangar ka iya rikidewa ta koma tashin hankali.

  • Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika
  • Goron Juma’a

Kungiyar ta bayyana hakan ne ta hannun Abdullahi Ismail, Sakatare na kungiyar reshen jihar Katsina a wata ganawa da ya yi da manema labarai.

ADVERTISEMENT

Ismail ya ce; “na zo nan domin mu yi kira ga matasa wadanda za a yi amfani da su domin cimma manufa; akan suna korafi da yunwa da tsanani na rayuwa dake damun al’umma. Bayan kuma wasu ne ke cusa musu wannan ra’ayin. Wanda a zahirin gaskiya abin ba nan ya dosa ba. Shiyasa muke kiran al’umma musamman matasanmu da ka da a yi amfani da su wajen yi ma gwamnati barna ko wajen kawo wani rudani a cikin kasa”, ya shawarce su.

Sannan ya ci gaba da cewa; “matasan na duba da irin kasashen Kenya da sauran kasashe da suke irin wannan zanga-zanga. Mutanen wadancan wuraren suna yi ne domin kasar su da ci gabanta. Amma mu a fahimtarmu wannan zanga-zangar da za a yi ba zanga-zanga ba ce ta ci gaban al’ummar Nijeriya, wasu ne suka kirkire shi domin cimma manufofinsu”, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Kungiyar ta ci gaba da cewa; “a kan haka, shugaban kungiyar tabbatar da dimokuradiyya a Nijeriya, Honorabul Abdurrahman Buba Kwacham, ya tara wannan taro ya kira mutane masu ruwa da tsaki a kan shugabanci na matasa da abin da ya shafi arewacin Nijeriya da ma kasar baki daya a kan a gaya wa mutane muhimmancin rashin shiga cikin wannan zanga-zanga da za a yi”.

Kungiyar ta ce zanga-zangar ba na gaskiya bane, na cimma wadansu manufofi ne. “Ba ana yi bane domin wahalar da kasar ke ciki. Idan domin matsalolin da kasa ke ciki ne, akwai shirye-shirye da yawa da gwamnati ta yi, domin magance wadannan matsalolin”, ya labarta.

Ya nesanta kungiyar da cewa gwamnati ta siye su ne su kashe kwarin guiwar matasan, inda ya jaddada cewa; gwamnati ba ta siye su ba; sai dai ya yarda cewa akwai damuwa ta rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fama da shi; “amma gwamnati na kan kokarin ganin ta magance wannan matsalolin. Hakan yasa muke ganin bai kamata matasa su sanya kansu a cikin wannan zanga-zanga ba”, ya lurantar.

Kungiyar ta ce ‘yancin gashin kai da aka bai wa kananan hukumomin Nijeriya, a ganin su tabbas zai magance matsaloli na tsaro sannan za a samu sauki; “domin ba sai sun jira gwamnatin jiha ko na tarayya ta kawo dauki ba. Domin suna da komai a hannunsu wanda za su yi amfani da shi domin magance matsalar tsaro domin taimaka ma al’umma”, in ji shi.

Da yake tabbatar da irin wahalar rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fuskanta ya ce; tabbas akwai matsaloli wanda ya hassala ‘yan Nijeriya, amma akwai wadanda za su yi amfani da zanga-zangar wajen cimma manufofinsu, “akwai wadanda za su zo su bi masu yin abin don Allah, masu yi domin ci gaban kasar, su shiga cikinsu su rika balla shagunan mutane suna kawo rudani a cikin al’umma. Wanda daga karshe duk zai tafi da sunan wannan zanga-zangar da aka shirya a kan yunwa da tsananin rayuwa, bayan kuma a zahiri ba haka bane.

Ya karkare da cewa; “muna yin abu ne domin kyautata rayuwar matasa. Muna shugabantar matasa ne. Hakan ya sa mu ka ga ya kyautu mu kira matasan nan mu sanar da su cewa wannan abin da suke yi idan suka tafi da shi, akwai wadanda za su shigo bata gari su canza ma abin tsari da kuduri wanda suke kan shi”, in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
Labarai

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Next Post
Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

LABARAI MASU NASABA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.