• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Kasa (NIS) ta yi kawance da takwararta ta duniya (IOM), da Hukumar Yaki Da Safarar Bil’adama (NAPTIP) da Sashen Ayyyukan Lafiya na PHS, wajen shirya wani taron kara wa juna sani da nufin samar da horo da dabarun aiki ga jami’anta.

An shirya horaswar ce a karkashin shirin da aka yi wa sunan TSI a takaice.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A wata sanarwa da Jami’in hulda da jama’a na NIS, Amos Okpu ya fitar, NIS ta bayyana cewa shirin yana samun tallafin hukumar kula da shige da fice ta duniya (IOM) da nufin bunkasa ayyuka a iyakokin kasa da kara sanya ido kan harkokin shige da fice a Nijeriya tare da taimaka wa hukumomin kula da shige da fice.

Shirin na da manufar bunkasa kwazo da hazakar jami’an da ke aiki a hukumomin dakile safarar mutane da shige da fice ta barauniyar hanya domin ayyuka su rika tafiya yadda ya dace a kowane lokaci.

NIS

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin karo na na biyu, Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere Idris, wanda ya samu wakilcin mataimakin kwanturola Janar mai kula da harkokin biza, Ishaka Abdulmumini Haliru, ya misalta kokarin abokan hukumar wajen kara bunkasa kwazon aikin jami’an NIS da NAPTIP a matsayin wani gagarumin ci gaba da zai kyautata harkokin shige da fice da dakile yawan safarar mutane ta barauniyar hanya, yana mai cewa hakan zai kara kyautata alaka a tsakanin bangarorin.

Ya ce, a kowani lokaci suna kula sosai da ba da fifiko ga sashin horar da jami’ansu domin tabbatar da ayyuka na gudana yadda ya dace, kan haka ne ma ya nuna farin cikinsa da wannan shirin.

NIS

A nata jawabin, darakta-janar ta Hukumar NAPTIP, Dakta Fatima Waziri-Azir, ta ce, IOM na tallafa wa shirye-shiryen da ke inganta kwazon jami’ai a fagen aiki a-kai-a-kai.

Ta yi kira ga hukumomi da jami’an da abin ya shafa da su yi amfani da wannan damar tallafin da suke samu daga kungiyoyin kasashen waje wajen inganta ayyukansu a kowani lokaci.

Sannan, ta bukaci jami’an NIS da NAPTIP da su ci gaba da kyautata alakar aiki mai inganci a tsakaninsu domin hada karfi da karfe waje guda don yaki da safarar mutane da jigila ta kai-komo ta barauniyar hanya.

Shi kuma a bangarensa, daraktan ayyukan lafiya na PHS, Dakta Geoffrey Okatubo, ya ce a ‘yan kwanakin baya sashen kula da lafiya ya fuskanci barazanar annobar korona da aka fuskanta, a yanzu kuma ga cutar kyandar biri (Monkey pox) da ake fama da ita a halin yanzu.

Sai ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da hadin guiwar abokan aiki na cikin kasar Nijeriya da kasashen waje ana samun sakamako mai kyau wajen kula da lafiya.

NIS

Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya sha nanata cewa zai mayar da hankali ga horas da jami’a domin inganta ayyukan hukumar a kowane sashe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Dan Nijeriya Ya Harbe Matarsa Da Kakarsa, Ya Kuma Kashe Kansa A Amurka

Next Post

Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Related

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
Labarai

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

12 minutes ago
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja
Labarai

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

2 hours ago
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
Labarai

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

3 hours ago
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
Labarai

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

3 hours ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Labarai

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

5 hours ago
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

7 hours ago
Next Post
Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Kwamitin tantance 'Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da 'Yan Takara 10 Cikin 23

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.