• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ki Amincewa A Mayar Da Shari’ar Abduljabbar Abuja

by Sadiq
3 years ago
Abduljabbar

Kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kano, ta ki amincewa da bukatar mayar da shari’ar Sheikh Abduljabbar Kabara zuwa babban birnin tarayya, Abuja.

Abduljabbar dai ya bukaci kotun da ta mayar da shari’ar tasa zuwa wata kotun a Abuja saboda zargin da yake na cewar kotun Kano ba za ta yi masa adalci ba.

  • Barazanar ‘Yan Bindiga: Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Duk Makarantun Jihar
  • Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

A yayin zaman kotun na yau Alhamis, wanda ya gudana karkashin mai shari’a Abdullahi Liman, lauyan Abduljabbar Nasir Kabara, Barista Dalhatu Shehu Usman, ya zargi alkalin kotun tarayyar na Kano da ganawa da kwamsihinan shari’a na Kano, Barista Musa Lawan a safiyar yau gabanin zaman kotun.

Wanda ya ce bisa ka’ida bai kamata a ce alkalin ya yi hakan ba, wanda kuma hakan yasa Sheikh Kabara ya karaya da cewar ba zai samu adalci a kotun ba.

Sai dai a wani martani da lauya gwamnati, Barista Dahiru Muhammad, ya kalubalanci wannan batu.

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Ya sanar da kotun cewar tun karfe 9 na safiyar yau, masu gabatar da karar suka ba shi kwafin wata sabuwar karar da suka shigar a Abuja na zargin take hakkinsa na dan adam, bayan batun na gaban alkalin wata kotu ta daban.

Daga nan ne mai shari’a Abdullahi Liman, ya ce ba zai rufe shari’ar ba, sannan a shari’ance babu inda aka ce bangare daya da ake shari’a da shi zai ce lallai shi ga kotun da yake bukata da ta saurari wata shari’ar.

Sannan ya umurci lauyan Abduljabbar da ya rubuto zargin da yake yi kan zuwan Kwamishinan shari’a na jihar Kano wajensa, tare da tabbatar da abin da suka tattauna na da alaka da shari’ar ta Abduljababr din ya shigar gabansa.

LEADERSHIP ta ruwaito a ranar 21 ga watan Yulin da muke ciki ne Shiekh Abduljabbar, ya garzaya kotun tarayyar da ke Kano, da bukatar a mayar da shari’ar da ake yi masa ta zargin batancin ga Annabi S.A.W zuwa ga wani alkalin daban.

Ya yi hakan ne saboda zargin cewar gwamantin Kano da Babbar Kotun Musulunci ta Kofar Kudu na take masa hakkinsa a matsayinsa na dan Adam.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Abduljabbar

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.