• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Ci Gaba Da Sanya Sarakuna Cikin Gudanar Da Shugabanci  – Gwamna Nasir

by Sulaiman and Umar Faruk
1 year ago
Kebbi

Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi ya tabbatar wa sarakunan gargajiya cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da sanya su cikin tsare-tsaren gudanar da mulki da kuma shirye -shiryen ci gaba don inganta rayuwar al’umma.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar al’ummar garin Besse ta kai masa ziyarar godiya a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi, domin nuna jin dadin nadin Farfesa Tijjani Muhammad Bande a matsayin sabon Uban kasar Besse (Barade na biyu) da ke karamar hukumar Koko-Besse.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Kasuwar Dodoru A Jihar Kebbi, Rumfuna Da Yawa Sun Lalace
  • Zanga-zanga: Daga Tutar Rasha Cin Amanar Kasa Ne – Janar Musa

Gwamna Nasir ya jaddada kudirin gwamnatinsa na shigar da Sarakunan cikin shirye-shiryen raya jihar da kasa baki daya, inda ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta amince da aikin gyaran hanyar Koko-Besse zuwa Zariya-Kalakala zuwa Bagudo, kuma nan ba da jimawa ba, za a fara aikin hanyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Ya kuma bayyana shirin bunkasa garuruwan yankin da sauran sassan jihar bayan kammala aikin gyaran fuska na babban birnin jihar. Ya kara da cewa, gwamnati za ta gyara makarantu 30 zuwa 50 a Koko-Besse domin inganta ilimi a yankin.

 

Har ilayau, Gwamnan ya taya Farfesa Bande murnar nadin da aka yi masa, inda ya bayyana shi a matsayin fitaccen malami kuma jami’in diflomasiyya wanda ya yi hasashe tare da daukaka martabar jihar Kebbi da Nijeriya a fagen kasa da kasa. Ya kuma bai wa Farfesa Bande tabbacin goyon bayansa wajen tafiyar da mulkin al’ummarsa cikin nasara.

 

Tun da farko, a jawabinsu, Uban kasa, kuma Dutsinmari, Alhaji Muhammadu Mu’allah’yidi Usman da Farfesa Abubakar Abdullahi Bagudo a madadin al’ummar Besse sun gode wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da nadin Farfesa Bande. Sun bayyana gamsuwarsu kan yadda Farfesa Bande zai iya yin amfani da kwarewarsa da iliminsa wajen bunkasa gundumar tare da yin kira ga gwamnan da ya ba sabon Uban kasar goyon baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Labarai

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
Manyan Labarai

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
Labarai

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Next Post
Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.