• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai
0
An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar kula da ayyuka ta Nijeriya (CIPMN), ta bayyana cewa ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya a halin yanzu sun kai sama da na naira tiriliyan 17.

 

Magatakardan cibiyar CIPMN, Mista Henry Mbadiwe ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja a wani taron manema labarai.

  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya
  • Kwazon Kasar Sin A Ayyukan Shiga Tsakani Na Samun Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa

Mbadiwe ya yi nuni da cewa, binciken ya nuna cewa manyan abubuwan da ke haifar da ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya sun hada da, “Rashin hangen nesa da rashin ingantaccen tsarin aikin daga farkon da rashin wadataccen kasafin kudin aikin da tsarin shari’a mara inganci da cin hanci da rashawa da hadin baki da kuma raunana cibiyoyi a Nijeriya wanda ke haifar da rashin ci gaba tare da sauye-sauye a harkokin siyasa.”

 

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

Ya tabbatar da cewa CIPMN za ta ci gaba da gudanar da sauye-sauyen gwamnatocin da suka shude da kuma gazawarsu tare da fara aiwatar da dokar da ta kafa cibiyar.

 

Ya ce, “Ba za mu iya ci gaba da zura ido ba muna kallon gwamnati tana barin irin wannan lamari ba.

 

“CIPMN za ta gudanar da canje-canjen gwamnatocin da suka gabata da inda suka samu rauni da kuma fara aiwatar sauye-sauye kamar yadda doka ta tanada.

 

“Za mu ci gaba da bin kadin dukkan ayyukan da aka fara aiwatarwa a Nijeriya, inda doka ta bukaci wadanda ke jagorantar wadannan ayyukan su kasance kwararrun manajojin ayyukan da CPMN ta ba su lasisi.”

 

Mbadiwe ya gargadi masu gudanar da ayyuka marasa lasisi a Nijeriya da su daina irin wannan aiki kai tsaye ko kuma su fuskanci sakamakon abin da suka aikatawa.

 

Ya ce, “Bari na bayyana muku cewa, cibiyar kula da gudanar da ayyuka ta Nijeriya ba za ta amince da manajojin ayyuka marasa lasisi suna kula da ayyuka a Nijeriya ba. Wadanda suke aikata hakan za su fuskanci mummunan hukunci.

 

“Dokar da ta kafa CIPMN ta bayyana cewa duk wanda ke cikin gwamnati da masu zaman kansu da ke shugabanta da jagorori da masu koyarwa fannin gudanar da ayyuka a Nijeriya dole ne a ba shi lasisin yin wannan sana’a.

 

“Ba shawara ba ce, doka ce, kuma muna tunanin lokaci ya yi da za mu fara bin doka a kasar nan.

 

“Daya daga cikin kalubalen da muke fuskanta a Nijeriya ba wai rashin dokoki ba ne, amma rashin mutunta wadannan dokoki ne, sau da yawa mutum zai aikata laifi kuma ya kauce wa hukunci.

 

“Duk da cewa ba mu da ikon kula da dukkan bangarorin, muna iya tabbatar muku da cewa a bangaren gudanar da ayyuka, mun himmatu wajen tabbatar da doka da oda, tare da tabbatar da cewa dukkan manajojin ayyukan suna da lasisi da kuma bin ka’idogin ayyukansu.”

 

Don haka, ya shawarci mutanen da suke da lasisin a fannin gudanar da ayyukan daga Cibiyar CIPMN da su tabbatar sun bi dokokin cibiyar yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaCin Hanci Da RashawaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Mutane Ke Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno

Next Post

Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Related

Kawayen amarya
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

2 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

5 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

6 hours ago
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

15 hours ago
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Labarai

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

16 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

16 hours ago
Next Post
Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.