ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
CIPMN

Cibiyar kula da ayyuka ta Nijeriya (CIPMN), ta bayyana cewa ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya a halin yanzu sun kai sama da na naira tiriliyan 17.

 

Magatakardan cibiyar CIPMN, Mista Henry Mbadiwe ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja a wani taron manema labarai.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya
  • Kwazon Kasar Sin A Ayyukan Shiga Tsakani Na Samun Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa

Mbadiwe ya yi nuni da cewa, binciken ya nuna cewa manyan abubuwan da ke haifar da ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya sun hada da, “Rashin hangen nesa da rashin ingantaccen tsarin aikin daga farkon da rashin wadataccen kasafin kudin aikin da tsarin shari’a mara inganci da cin hanci da rashawa da hadin baki da kuma raunana cibiyoyi a Nijeriya wanda ke haifar da rashin ci gaba tare da sauye-sauye a harkokin siyasa.”

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya tabbatar da cewa CIPMN za ta ci gaba da gudanar da sauye-sauyen gwamnatocin da suka shude da kuma gazawarsu tare da fara aiwatar da dokar da ta kafa cibiyar.

 

Ya ce, “Ba za mu iya ci gaba da zura ido ba muna kallon gwamnati tana barin irin wannan lamari ba.

 

“CIPMN za ta gudanar da canje-canjen gwamnatocin da suka gabata da inda suka samu rauni da kuma fara aiwatar sauye-sauye kamar yadda doka ta tanada.

 

“Za mu ci gaba da bin kadin dukkan ayyukan da aka fara aiwatarwa a Nijeriya, inda doka ta bukaci wadanda ke jagorantar wadannan ayyukan su kasance kwararrun manajojin ayyukan da CPMN ta ba su lasisi.”

 

Mbadiwe ya gargadi masu gudanar da ayyuka marasa lasisi a Nijeriya da su daina irin wannan aiki kai tsaye ko kuma su fuskanci sakamakon abin da suka aikatawa.

 

Ya ce, “Bari na bayyana muku cewa, cibiyar kula da gudanar da ayyuka ta Nijeriya ba za ta amince da manajojin ayyuka marasa lasisi suna kula da ayyuka a Nijeriya ba. Wadanda suke aikata hakan za su fuskanci mummunan hukunci.

 

“Dokar da ta kafa CIPMN ta bayyana cewa duk wanda ke cikin gwamnati da masu zaman kansu da ke shugabanta da jagorori da masu koyarwa fannin gudanar da ayyuka a Nijeriya dole ne a ba shi lasisin yin wannan sana’a.

 

“Ba shawara ba ce, doka ce, kuma muna tunanin lokaci ya yi da za mu fara bin doka a kasar nan.

 

“Daya daga cikin kalubalen da muke fuskanta a Nijeriya ba wai rashin dokoki ba ne, amma rashin mutunta wadannan dokoki ne, sau da yawa mutum zai aikata laifi kuma ya kauce wa hukunci.

 

“Duk da cewa ba mu da ikon kula da dukkan bangarorin, muna iya tabbatar muku da cewa a bangaren gudanar da ayyuka, mun himmatu wajen tabbatar da doka da oda, tare da tabbatar da cewa dukkan manajojin ayyukan suna da lasisi da kuma bin ka’idogin ayyukansu.”

 

Don haka, ya shawarci mutanen da suke da lasisin a fannin gudanar da ayyukan daga Cibiyar CIPMN da su tabbatar sun bi dokokin cibiyar yadda ya kamata.

CIPMN
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
CIPMN
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.