ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
CIPMN

Cibiyar kula da ayyuka ta Nijeriya (CIPMN), ta bayyana cewa ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya a halin yanzu sun kai sama da na naira tiriliyan 17.

 

Magatakardan cibiyar CIPMN, Mista Henry Mbadiwe ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja a wani taron manema labarai.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya
  • Kwazon Kasar Sin A Ayyukan Shiga Tsakani Na Samun Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa

Mbadiwe ya yi nuni da cewa, binciken ya nuna cewa manyan abubuwan da ke haifar da ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya sun hada da, “Rashin hangen nesa da rashin ingantaccen tsarin aikin daga farkon da rashin wadataccen kasafin kudin aikin da tsarin shari’a mara inganci da cin hanci da rashawa da hadin baki da kuma raunana cibiyoyi a Nijeriya wanda ke haifar da rashin ci gaba tare da sauye-sauye a harkokin siyasa.”

 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya tabbatar da cewa CIPMN za ta ci gaba da gudanar da sauye-sauyen gwamnatocin da suka shude da kuma gazawarsu tare da fara aiwatar da dokar da ta kafa cibiyar.

 

Ya ce, “Ba za mu iya ci gaba da zura ido ba muna kallon gwamnati tana barin irin wannan lamari ba.

 

“CIPMN za ta gudanar da canje-canjen gwamnatocin da suka gabata da inda suka samu rauni da kuma fara aiwatar sauye-sauye kamar yadda doka ta tanada.

 

“Za mu ci gaba da bin kadin dukkan ayyukan da aka fara aiwatarwa a Nijeriya, inda doka ta bukaci wadanda ke jagorantar wadannan ayyukan su kasance kwararrun manajojin ayyukan da CPMN ta ba su lasisi.”

 

Mbadiwe ya gargadi masu gudanar da ayyuka marasa lasisi a Nijeriya da su daina irin wannan aiki kai tsaye ko kuma su fuskanci sakamakon abin da suka aikatawa.

 

Ya ce, “Bari na bayyana muku cewa, cibiyar kula da gudanar da ayyuka ta Nijeriya ba za ta amince da manajojin ayyuka marasa lasisi suna kula da ayyuka a Nijeriya ba. Wadanda suke aikata hakan za su fuskanci mummunan hukunci.

 

“Dokar da ta kafa CIPMN ta bayyana cewa duk wanda ke cikin gwamnati da masu zaman kansu da ke shugabanta da jagorori da masu koyarwa fannin gudanar da ayyuka a Nijeriya dole ne a ba shi lasisin yin wannan sana’a.

 

“Ba shawara ba ce, doka ce, kuma muna tunanin lokaci ya yi da za mu fara bin doka a kasar nan.

 

“Daya daga cikin kalubalen da muke fuskanta a Nijeriya ba wai rashin dokoki ba ne, amma rashin mutunta wadannan dokoki ne, sau da yawa mutum zai aikata laifi kuma ya kauce wa hukunci.

 

“Duk da cewa ba mu da ikon kula da dukkan bangarorin, muna iya tabbatar muku da cewa a bangaren gudanar da ayyuka, mun himmatu wajen tabbatar da doka da oda, tare da tabbatar da cewa dukkan manajojin ayyukan suna da lasisi da kuma bin ka’idogin ayyukansu.”

 

Don haka, ya shawarci mutanen da suke da lasisin a fannin gudanar da ayyukan daga Cibiyar CIPMN da su tabbatar sun bi dokokin cibiyar yadda ya kamata.

CIPMN
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
CIPMN
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.