• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
12 months ago
in Labarai
0
Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana da masu ruwa da tsaki a lamuran da suka shafi noma sun bayyana muhimman dalilin da suka sabbaba Nijeriya ke tsintar kanta cikin matsalolin karancin abinci.

 

Masanan sun ce a baya dai, bangaren noma shi ke jan ragamar tattalin arzikin Nijeriya, yayin da manoma a jihohi da shiyyoyi suka maida hankali ka-in-da-na-in wajen noma kayan abinci a yankunansu da hakan ya bayar da damar wadata garuruwansu da kayan abinci har ma su fitar zuwa waje.

  • Nazari Kan Samun Kudin Shiga Ta Hanyar Kiwon Kajin Gida
  • Masana Sun Nuna Damuwarsu Kan Yadda Ake Takura Wa Masu Zuba Jari Da Ka’idoji

Sun kuma yi la’akari da yadda manoman arewa suka fi kwarewa wajen noma shinkafa, masara, gyada kuma wadannan abincin ana samar da su sosai, wadanda su ne ma aka fi amfani da su, yayin da a kudu maso yamma kuma suka gwanance wajen noman koko da rogo, inda yankin kudu maso gabas suka rungumi samar da manja.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

A cewar masanan, kasar ta samu kanta cikin cin gajiyar wadannan abubuwan da ake noma, amma yanzu lamarin na neman zama babbar matsala, inda ake samun karancin abinci, yayin da manoma da dama suka daina noma, kamfanoni su na fuskantar karancin samun kayayyakin amfani, sannan ita kuma gwamnati ta dukufa wajen yaki da matsalar tsaro da rigingimun siyasa.

 

Shugaban kungiyar manoma ta COMAFAS, Dakta Austine Maduka, ya ce, samun danyen mai da ake yi a Nijeriya ya sanya kasar ta sakankance da lamarin samar da kayan noma, inda ya ce, hakan kuma ya janyo matasa da dama sun bar garuruwansu da ke kauyuka domin zuwa birane neman aiki a bangaren mai da iskar gas, yayin da suka bar harkokin noma kuma.

 

Ya kuma nuna cewa rashin nagartattun tsare-tsaren gwamnati kan noma sun kara shafan lamarin samar da kayan abinci. Ya nuna takaicinsa, kan yadda shugabannin da aka yi a Nijeriya ba su iya ci gaba da tafiyar da tsare-tsaren shugabannin da suka karbi mulki a hannunsu, inda ya nuna cewa kowani shugaba ya zo sai ya ce zai yi nasa tsarin daban, yayin da hakan ke maida hannun agogo baya.

 

Ya kuma nuna cewa wasu shugabannin sun fi maida hankali kan nau’ikan kayan abinci da ake cirewa a arewa, yayin da wasu tsare-tsaren gwamnatocin baya kuma suka fi daukan hankali a irin kayan abincin da ake nomawa a kudanci.

 

Kazalika, ya nemi gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar ruwa da ta bude wasu karin dam-dam da manoma za suke samun ruwa a kowace shekara yadda suke bukata. Ya ce, kacokam an dogara ne kawai da noma in an samu damina, yayin da noman rani kuma ba su da yawa.

 

Ya ce, ya kamata gwamnati ta tanada ruwan da ke malala a kasa, musamman wanda yake zama ambaliya ta yadda manoma za su samu na amfani da shi bayan damina, sannan ta kara samar da filayen noma a jihohi da kananan hukumomi.

 

Sai ya nuna cewa wasu gwamnonin su na kokari sosai wajen taimaka wa harkokin manoma da dukkanin abubuwan da ake bukatu a bangaren noma, ya buga misali da Jihar Jigawa, ya ce kokarin da gwamnatin Jigawa ke yi a bangaren noma za a ga alfanunsa nan gaba.

 

Ya ce, gwamnatin Inugu da Anambra su ma a kwanan nan sun rabar wa manoma da iri da kayan noma. Ya ce, akwai bukatar gwamnatoci su sanya a ransu wajen maida hankali kan yadda za a yi noma da yadda za a girbe amfanin noma.

 

A nasa bangaren, kwararre kan noman rogo daga Jihar Ogun, Kunle Abdul ya soki gwamnatin jihar da rashin kyawawan tsare-tsaren da za su ciyar da harkokin noma gaba, inda ta kasa koyi da yunkurin gwamnatin tarayya na inganta harkokin noma.

 

Shi kuwa, kwararre kan abinci da wadatar abinci, Hammed Jimoh ya ce, manyan matsalolin da Nijeriya ke fuskanta a bangaren samar da abinci sun hada har da matsalar rashin tsaro da ya janyo salwantuwar manoma da dama a kasar nan, musamman a jihohin Borno, Benuwai, Zamfara, Kaduna da sauran jihohi, lamarin da ke kara sanyawa wasu manoma kaurace wa gonakai domin tsira da rayukansu.

 

“Idan kuka nazarci yankunan da matsalolin tsaro suka fi kamari a halin yanzu a Nijeriya, za a fahimci jihohin nan su ne masu samar da abinci mafi yawa a baya, kamar jihohin Borno, Katsina, Kaduna da Benuwai.”

 

Jimoh ya kuma ce sauyin yanayi shi ma na barazana ga wadatar samar da abinci a Nijeriya, “An fi dogara da ruwan damina wajen noma a Nijeriya, sauyin yanayi na canzawa. An gaya min cewa kudu maso yamma kusan sama da watanni biyu ba su samu ruwan sama ba, don haka yanayin na canzawa.

 

“Muddin in za mu dogara kacokam kan sai mun samu ruwan sama mu yi noma, gaskiya za mu yi ta samun matsala, saboda ba za mu dunga samun abun da muke so ba, yana da kyau a nemo wasu hanyoyin na daban.”

 

Wani manomi a Jihar Kogi, Sunday Audu ya zargi gwamnatin da kin taimaka wa manoma balle manoma su samu kyautata nomansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno

Next Post

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

Related

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

3 hours ago
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Labarai

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

4 hours ago
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

5 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

8 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

16 hours ago
Next Post
A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.