ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Sojoji

A wasu hare-hare da dakarun sojin Nijeriya suka kai wa ‘yan ta’adda sun yi nasarar hallaka biyar tare da karbar wasu ‘yan ta’adda da iyalai 44 da suka mika wuya a jihar Borno.

 

Sojojin sun kuma kama wani kasurgumin barawon shanu da ake nema ruwa a jallo a Jihar Filato da kuma wani da ake zargin mai sayar da makamai ne a jihar Oyo.

ADVERTISEMENT
  • Tsadar Rayuwa A Nijeriya Ta Karu Da Kashi 19 A Wata 1
  • Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

Sakamakon wadannan hare-hare, sojojin sun kuma kwato bama-bamai, makamai, alburusai, da shanun da aka sace.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta fitar a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa, a ranar 12 ga watan Agustan shekarar 2024 ne sojojin suka kai wani samame a wani sansani na ‘yan ta’addan ISWAP a karamar hukumar Bama ta jihar Borno inda suka kashe ‘yan ta’adda biyar. Sun kuma kwato Bama-bamai guda biyu, bindigogin toka guda biyu, abin durin Bomb na RPG daya, Kwanson alburushi na bindigar AK-47 Rifle daya, harsashi 23 samfurin 7.62 d 54mm, babura shida da magunguna iri-iri.

 

A ci gaba da farmakin da ake kai wa kungiyoyin ‘yan ta’adda a fagen yaki na Arewa-maso-Gabas, “’yan ta’addan Boko Haram 44 da iyalansu sun kuma mika wuya ga sojojin da aka tura a kananan hukumomin Bama, Dikwa da Gwoza na Jihar Borno”.

 

A halin da ake ciki kuma, sojoji a Jihar Filato sun kama wani da ake zargi da satar shanu, Malam Maawuya Shuaibu, a Mararaban Kantom da ke karamar hukumar Barikin Ladi a jihar.

 

An kama wanda ake zargin wanda ya kasance cikin jerin sunayen mutanen da jami’an tsaro ke nema bisa alaka da aikata miyagun laifuka a kananan hukumomin Barikin Ladi, Riyom da Mangu na jihar, yayin da sojojin suka dauki mataki bayan samun sahihan bayanan sirri a kan wanda ake zargin. Dakarun sun kwato shanu 32 daga hannun wanda ake zargin.

 

Bugu da kari, a Jihar Bayelsa, sojoji sun kai samame a maboyar miyagu da ake zargin ‘yan fashi ne a yankin Korokorosie da ke karamar hukumar kudancin Ijaw, inda suka kama wani mai suna Donald Emason tare da kwato bindigar Ribarbar guda daya da wasu bindigogi kirar gida guda biyu da wanda ake zargin ya boye.

 

Hakazalika, sojojin da aka tura karamar hukumar Akinyele ta jihar Oyo, sun kama wani da ake zargin dan bindiga ne Mohammed Bello, mai shekaru 33.

 

Sanarwar ta kuma ce wanda ake zargin, wanda aka cafko shi daga maboyarsa, “ya amsa cewa yana daya daga cikin masu aika makamai da alburusai ga gungun masu garkuwa da mutane na Bello Chikidawoje da ke aikata miyagun ayyukansu a yankin baki daya”.

Sojoji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Sojoji
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.