ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Sojoji

A wasu hare-hare da dakarun sojin Nijeriya suka kai wa ‘yan ta’adda sun yi nasarar hallaka biyar tare da karbar wasu ‘yan ta’adda da iyalai 44 da suka mika wuya a jihar Borno.

 

Sojojin sun kuma kama wani kasurgumin barawon shanu da ake nema ruwa a jallo a Jihar Filato da kuma wani da ake zargin mai sayar da makamai ne a jihar Oyo.

ADVERTISEMENT
  • Tsadar Rayuwa A Nijeriya Ta Karu Da Kashi 19 A Wata 1
  • Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

Sakamakon wadannan hare-hare, sojojin sun kuma kwato bama-bamai, makamai, alburusai, da shanun da aka sace.

 

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta fitar a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa, a ranar 12 ga watan Agustan shekarar 2024 ne sojojin suka kai wani samame a wani sansani na ‘yan ta’addan ISWAP a karamar hukumar Bama ta jihar Borno inda suka kashe ‘yan ta’adda biyar. Sun kuma kwato Bama-bamai guda biyu, bindigogin toka guda biyu, abin durin Bomb na RPG daya, Kwanson alburushi na bindigar AK-47 Rifle daya, harsashi 23 samfurin 7.62 d 54mm, babura shida da magunguna iri-iri.

 

A ci gaba da farmakin da ake kai wa kungiyoyin ‘yan ta’adda a fagen yaki na Arewa-maso-Gabas, “’yan ta’addan Boko Haram 44 da iyalansu sun kuma mika wuya ga sojojin da aka tura a kananan hukumomin Bama, Dikwa da Gwoza na Jihar Borno”.

 

A halin da ake ciki kuma, sojoji a Jihar Filato sun kama wani da ake zargi da satar shanu, Malam Maawuya Shuaibu, a Mararaban Kantom da ke karamar hukumar Barikin Ladi a jihar.

 

An kama wanda ake zargin wanda ya kasance cikin jerin sunayen mutanen da jami’an tsaro ke nema bisa alaka da aikata miyagun laifuka a kananan hukumomin Barikin Ladi, Riyom da Mangu na jihar, yayin da sojojin suka dauki mataki bayan samun sahihan bayanan sirri a kan wanda ake zargin. Dakarun sun kwato shanu 32 daga hannun wanda ake zargin.

 

Bugu da kari, a Jihar Bayelsa, sojoji sun kai samame a maboyar miyagu da ake zargin ‘yan fashi ne a yankin Korokorosie da ke karamar hukumar kudancin Ijaw, inda suka kama wani mai suna Donald Emason tare da kwato bindigar Ribarbar guda daya da wasu bindigogi kirar gida guda biyu da wanda ake zargin ya boye.

 

Hakazalika, sojojin da aka tura karamar hukumar Akinyele ta jihar Oyo, sun kama wani da ake zargin dan bindiga ne Mohammed Bello, mai shekaru 33.

 

Sanarwar ta kuma ce wanda ake zargin, wanda aka cafko shi daga maboyarsa, “ya amsa cewa yana daya daga cikin masu aika makamai da alburusai ga gungun masu garkuwa da mutane na Bello Chikidawoje da ke aikata miyagun ayyukansu a yankin baki daya”.

Sojoji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Sojoji
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.