ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Abinci

Masana da masu ruwa da tsaki a lamuran da suka shafi noma sun bayyana muhimman dalilin da suka sabbaba Nijeriya ke tsintar kanta cikin matsalolin karancin abinci.

 

Masanan sun ce a baya dai, bangaren noma shi ke jan ragamar tattalin arzikin Nijeriya, yayin da manoma a jihohi da shiyyoyi suka maida hankali ka-in-da-na-in wajen noma kayan abinci a yankunansu da hakan ya bayar da damar wadata garuruwansu da kayan abinci har ma su fitar zuwa waje.

ADVERTISEMENT
  • Nazari Kan Samun Kudin Shiga Ta Hanyar Kiwon Kajin Gida
  • Masana Sun Nuna Damuwarsu Kan Yadda Ake Takura Wa Masu Zuba Jari Da Ka’idoji

Sun kuma yi la’akari da yadda manoman arewa suka fi kwarewa wajen noma shinkafa, masara, gyada kuma wadannan abincin ana samar da su sosai, wadanda su ne ma aka fi amfani da su, yayin da a kudu maso yamma kuma suka gwanance wajen noman koko da rogo, inda yankin kudu maso gabas suka rungumi samar da manja.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A cewar masanan, kasar ta samu kanta cikin cin gajiyar wadannan abubuwan da ake noma, amma yanzu lamarin na neman zama babbar matsala, inda ake samun karancin abinci, yayin da manoma da dama suka daina noma, kamfanoni su na fuskantar karancin samun kayayyakin amfani, sannan ita kuma gwamnati ta dukufa wajen yaki da matsalar tsaro da rigingimun siyasa.

 

Shugaban kungiyar manoma ta COMAFAS, Dakta Austine Maduka, ya ce, samun danyen mai da ake yi a Nijeriya ya sanya kasar ta sakankance da lamarin samar da kayan noma, inda ya ce, hakan kuma ya janyo matasa da dama sun bar garuruwansu da ke kauyuka domin zuwa birane neman aiki a bangaren mai da iskar gas, yayin da suka bar harkokin noma kuma.

 

Ya kuma nuna cewa rashin nagartattun tsare-tsaren gwamnati kan noma sun kara shafan lamarin samar da kayan abinci. Ya nuna takaicinsa, kan yadda shugabannin da aka yi a Nijeriya ba su iya ci gaba da tafiyar da tsare-tsaren shugabannin da suka karbi mulki a hannunsu, inda ya nuna cewa kowani shugaba ya zo sai ya ce zai yi nasa tsarin daban, yayin da hakan ke maida hannun agogo baya.

 

Ya kuma nuna cewa wasu shugabannin sun fi maida hankali kan nau’ikan kayan abinci da ake cirewa a arewa, yayin da wasu tsare-tsaren gwamnatocin baya kuma suka fi daukan hankali a irin kayan abincin da ake nomawa a kudanci.

 

Kazalika, ya nemi gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar ruwa da ta bude wasu karin dam-dam da manoma za suke samun ruwa a kowace shekara yadda suke bukata. Ya ce, kacokam an dogara ne kawai da noma in an samu damina, yayin da noman rani kuma ba su da yawa.

 

Ya ce, ya kamata gwamnati ta tanada ruwan da ke malala a kasa, musamman wanda yake zama ambaliya ta yadda manoma za su samu na amfani da shi bayan damina, sannan ta kara samar da filayen noma a jihohi da kananan hukumomi.

 

Sai ya nuna cewa wasu gwamnonin su na kokari sosai wajen taimaka wa harkokin manoma da dukkanin abubuwan da ake bukatu a bangaren noma, ya buga misali da Jihar Jigawa, ya ce kokarin da gwamnatin Jigawa ke yi a bangaren noma za a ga alfanunsa nan gaba.

 

Ya ce, gwamnatin Inugu da Anambra su ma a kwanan nan sun rabar wa manoma da iri da kayan noma. Ya ce, akwai bukatar gwamnatoci su sanya a ransu wajen maida hankali kan yadda za a yi noma da yadda za a girbe amfanin noma.

 

A nasa bangaren, kwararre kan noman rogo daga Jihar Ogun, Kunle Abdul ya soki gwamnatin jihar da rashin kyawawan tsare-tsaren da za su ciyar da harkokin noma gaba, inda ta kasa koyi da yunkurin gwamnatin tarayya na inganta harkokin noma.

 

Shi kuwa, kwararre kan abinci da wadatar abinci, Hammed Jimoh ya ce, manyan matsalolin da Nijeriya ke fuskanta a bangaren samar da abinci sun hada har da matsalar rashin tsaro da ya janyo salwantuwar manoma da dama a kasar nan, musamman a jihohin Borno, Benuwai, Zamfara, Kaduna da sauran jihohi, lamarin da ke kara sanyawa wasu manoma kaurace wa gonakai domin tsira da rayukansu.

 

“Idan kuka nazarci yankunan da matsalolin tsaro suka fi kamari a halin yanzu a Nijeriya, za a fahimci jihohin nan su ne masu samar da abinci mafi yawa a baya, kamar jihohin Borno, Katsina, Kaduna da Benuwai.”

 

Jimoh ya kuma ce sauyin yanayi shi ma na barazana ga wadatar samar da abinci a Nijeriya, “An fi dogara da ruwan damina wajen noma a Nijeriya, sauyin yanayi na canzawa. An gaya min cewa kudu maso yamma kusan sama da watanni biyu ba su samu ruwan sama ba, don haka yanayin na canzawa.

 

“Muddin in za mu dogara kacokam kan sai mun samu ruwan sama mu yi noma, gaskiya za mu yi ta samun matsala, saboda ba za mu dunga samun abun da muke so ba, yana da kyau a nemo wasu hanyoyin na daban.”

 

Wani manomi a Jihar Kogi, Sunday Audu ya zargi gwamnatin da kin taimaka wa manoma balle manoma su samu kyautata nomansu.

Abinci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Abinci
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.