• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Su Riƙa Bayar Da Rahoton Gaskiya Kan Nijeriya

by Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Su Riƙa Bayar Da Rahoton Gaskiya Kan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na ƙasa da ƙasa da su riƙa bin ƙa’idojin adalci da sahihanci a cikin rahotannin su da suka shafi Nijeriya.

 

Idris ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin wata tawaga daga BBC a ofishin sa a ranar Alhamis.

  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno
  • Al’ummar Arewa: Bango Ne Ya Tsage Kadangare Ya Samu Wurin Shiga

A wata sanarwa da Mataimakin Ministan na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar, an bayyana cewa ministan ya ce yayin da manufofin gwamnatin Tinubu ke ci gaba da tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida, gwamnati na sa ran ƙungiyoyin yaɗa labaran duniya su tabbatar da gaskiya da adalci a cikin rahotonnin su.

 

Labarai Masu Nasaba

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Ministan ya jaddada muhimmancin daidaito da rashin son kai wajen bayar da rahotanni, kuma ya bayyana cewa yayin da Nijeriya, kamar kowace ƙasa, take fuskantar ƙalubale, yana da matuƙar muhimmanci kafafen yaɗa labarai na duniya su ba da cikakken bayani, maimakon mayar da hankali kan abubuwa marasa kyau.

 

Ya ce, “Za mu kuma roƙe ku da ku ci gaba da daidaita labaran ku don jin ta bakin mu kan labari. Ba kawai munanan abubuwan da ke fitowa daga Nijeriya ba, akwai abubuwa masu kyau da yawa kuma na tabbata wakilan ku da ke nan sun ga cewa muna da abubuwa masu kyau da muke yi a ƙasar nan kuma akwai cigaba zuwa ga wadata da muke gani.

 

“Ina so in bayyana maku ƙudirin gwamnatin Nijeriya ga kowace ƙungiya mai tattara labarai. Ƙudurin mu shi ne cewa muna son mu kasance cikin mai da hankali da rashin son zuciya kuma cikin ‘yanci.”

 

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin Nijeriya ba ta samu wani rahoto da ya shafi cin zarafin ‘yan jarida da ke aiki da kafafen yaɗa labarai na duniya a ƙasar ba.

 

Ya ce, “Manufar gwamnatin Tinubu ita ce kowace ƙungiya ta labarai tana da ‘yancin gudanar da wannan sana’a kuma ina farin ciki da ba ku kawo mana rahoton wani ma’aikacin ku ba, wanda aka ci zarafin sa ko kuma ya fuskanci matsin lamba daga gwamnatin Nijeriya ba.”

 

Idris ya yaba wa irin hazaƙar da BBC ta yi wajen mayar da ɗakin watsa labarai na Sashen Hausa daga birnin Landan zuwa Abuja, inda masu kallo da kasuwanni suke, yana mai jaddada cewa wannan gagarumin shiri ya sa aka haɗa ‘yan Nijeriya kusan 200 da ke aiki da BBC a faɗin ƙasar.

 

Ministan ya bayyana jin daɗin sa da ɗorewar amana da mutunta juna tsakanin BBC da masu saurare a Nijeriya, dangantakar da ke da ƙarfi tun kusan shekaru 60.

 

Ya ce, “Haƙiƙa al’ummar Nijeriya abokan haɗin gwiwa ne da BBC kuma wannan ƙawancen ya fara shekaru da dama da suka wuce kuma ba a daina wannan sadaukarwar da muka ji a BBC da kuma mutuntawa da amincewar mutanen mu tun shekaru biyar zuwa sittin da suka gabata.”

 

Ya jinjina wa BBC kan yadda ta fara aikin gina ƙwarewar wasu ‘yan jarida da ke aiki da ƙungiyoyin yaɗa labarai na gwamnati, ya kuma yi kira ga BBC da su yi makamancin hakan ga kafafen yaɗa labarai masu zaman kan su.

 

A nasa jawabin, Daraktan Labaran Duniya kuma Mataimakin Shugaban BBC, Mista Jonathan Munro, wanda ya zo Nijeriya a karon farko, ya ce ya yi matuƙar farin ciki da shaharar BBC a ƙasar.

 

Ya ce BBC ta faɗaɗa zuwa kafofin watsa labarai da yawa a Nijeriya kuma yanzu tana yaɗa shirye-shiryen ta a cikin harsunan Pijin da Hausa da Ibo da kuma Yarbanci domin isa ga masu sauraro daban-daban a ƙasar.

 

Mista Munro, wanda ya bayyana Nijeriya a matsayin ƙasa mai ƙarfin faɗa-a-ji a duniya, ya ce kimanin mutane miliyan 30 ne ke ziyartar sashen labarai na BBC a Nijeriya a duk mako, wanda hakan ya sa Nijeriya ta zama ta uku a duniya wajen tallata BBC bayan Amurka da Indiya.

 

Mista Munro ya samu rakiyar Shugaban Harsunan Yammacin Afirka, Ehizojie Okharadia; Shugaban Sashen Labarai na Afirka, Juliet Njeri, da Shugaban Sashen Hausa na BBC, Malam Aliyu Tanko.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NBCVOA
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

Next Post

Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

Related

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

35 minutes ago
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Labarai

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

2 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

3 hours ago
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

16 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

21 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

22 hours ago
Next Post
Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

LABARAI MASU NASABA

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.