• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Tafi Faransa A Sabon Jirgin Da Aka Saya Masa

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Tafi Faransa A Sabon Jirgin Da Aka Saya Masa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya tafi Faransa a sabon jirgin Airbus A330 da aka saya masa a cewar fadar shugaban kasa.

Jirgin ya maye gurbin tsohon da shugabannin Najeriya suka kwashe shekaru 19 ana amfani da shi in ji Kakakin Tinubu Bayo Onanuga.

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Karuwar Zargin Cin Zarafi A Rundunar Sojojin Amurka
  • Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Vietnam

“Wannan sabon jirgi da aka sayo a farashi mai rahusa, ya sa Najeriya za ta kauce wa kashe miliyoyin daloli wajen gyara da sayen mai a kowace shekara.” Onanuga ya ce a wani sako da ya wallafa a shafin Twitter a ranar Litinin.

Tun a zamanin tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo ake amfani da tsohon jirgin a cewar shi.

Maye gurbin tsohon jirgin mai lamba B737 – 700 (BBJ) ya biyo bayan zaman jin bahasi da majalisar dokokin Najeriya ta yi kan lafiyar jirgin da kuma kudin gyaransa, “musamman bayan da ya lalace yayin wata tafiya da aka yi da shi zuwa Saudiyya.”

Labarai Masu Nasaba

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sabon jirgin ya iso Abuja ne, daren ranar Lahadi, bayan kamfanin China da ya sa kotu ta kwace shi, ya amince ya saki guda daya da zai kai shugaba Tinubu Faransa.

Jirgin kirar 330 na daga cikin kadarorin wani attajirin da ke harkar mai ya mika shi ga bankin Jamus, a matsayin jinginar karbar lamuni, daga bisani kuma aka sayar da shi.

Bayanai sun ce wani kamfanin sufurin jiragen Amurka da ake kira L&L da ke Miami Florida ne, ya jagoranci yarjejeniyar sayar wa Nijeriya jirgin a kan sama da dala miliyan 100.

Wasu rahotanni sun bayyana cewar Nijeriya ta samu jirgin a farashi mai sauki domin a yanzu farashinsa ya kai Dala miliyan 600.

Kasaitaccen jirgin na alfarma yanzu ya zama jirgin shugaban kasa da ake kira ‘Nigeria Air Force One’ mai lamba 5N-NGA.

Wata majiya daga fadar shugaban kasa, ta ce sabon jirgin ya ci kudinsa saboda kayan alatun da ke ciki da kuma inagancinsa la’akari da girma da kuma kimar shugaban Nijeriya a idon duniya.

A baya dai an tafka mahawara a kan muhimmancin sauyawa shugaban kasa jirgi, ya yin da babu wani bayani daga fadar shugaban kasa dangane da wannan ciniki.

A baya’yan Nijeriya sun bayyana bacin ransu dangane da bukatar sayen sabon jirgin da Tinubu ya yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jirgin SamaJirgin Shugaban KasaNigeria Airforce OneTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NNPC Ba Ya Biyan Tallafin Man Fetur – Ajiya

Next Post

NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

Related

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

51 seconds ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

15 hours ago
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 
Labarai

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

17 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Watsi Ga Ƙarin Girma Ga ASP 179, Ta Ɗaga Darajar 952 Zuwa DSP

19 hours ago
Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 
Manyan Labarai

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

20 hours ago
Next Post
NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

LABARAI MASU NASABA

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

August 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

August 20, 2025
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

August 20, 2025
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

August 20, 2025
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

August 20, 2025
Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

August 20, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Watsi Ga Ƙarin Girma Ga ASP 179, Ta Ɗaga Darajar 952 Zuwa DSP

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.