ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Tafi Faransa A Sabon Jirgin Da Aka Saya Masa

by Sadiq
2 years ago
Jirgin

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya tafi Faransa a sabon jirgin Airbus A330 da aka saya masa a cewar fadar shugaban kasa.

Jirgin ya maye gurbin tsohon da shugabannin Najeriya suka kwashe shekaru 19 ana amfani da shi in ji Kakakin Tinubu Bayo Onanuga.

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Karuwar Zargin Cin Zarafi A Rundunar Sojojin Amurka
  • Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Vietnam

“Wannan sabon jirgi da aka sayo a farashi mai rahusa, ya sa Najeriya za ta kauce wa kashe miliyoyin daloli wajen gyara da sayen mai a kowace shekara.” Onanuga ya ce a wani sako da ya wallafa a shafin Twitter a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Tun a zamanin tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo ake amfani da tsohon jirgin a cewar shi.

Maye gurbin tsohon jirgin mai lamba B737 – 700 (BBJ) ya biyo bayan zaman jin bahasi da majalisar dokokin Najeriya ta yi kan lafiyar jirgin da kuma kudin gyaransa, “musamman bayan da ya lalace yayin wata tafiya da aka yi da shi zuwa Saudiyya.”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

Sabon jirgin ya iso Abuja ne, daren ranar Lahadi, bayan kamfanin China da ya sa kotu ta kwace shi, ya amince ya saki guda daya da zai kai shugaba Tinubu Faransa.

Jirgin kirar 330 na daga cikin kadarorin wani attajirin da ke harkar mai ya mika shi ga bankin Jamus, a matsayin jinginar karbar lamuni, daga bisani kuma aka sayar da shi.

Bayanai sun ce wani kamfanin sufurin jiragen Amurka da ake kira L&L da ke Miami Florida ne, ya jagoranci yarjejeniyar sayar wa Nijeriya jirgin a kan sama da dala miliyan 100.

Wasu rahotanni sun bayyana cewar Nijeriya ta samu jirgin a farashi mai sauki domin a yanzu farashinsa ya kai Dala miliyan 600.

Kasaitaccen jirgin na alfarma yanzu ya zama jirgin shugaban kasa da ake kira ‘Nigeria Air Force One’ mai lamba 5N-NGA.

Wata majiya daga fadar shugaban kasa, ta ce sabon jirgin ya ci kudinsa saboda kayan alatun da ke ciki da kuma inagancinsa la’akari da girma da kuma kimar shugaban Nijeriya a idon duniya.

A baya dai an tafka mahawara a kan muhimmancin sauyawa shugaban kasa jirgi, ya yin da babu wani bayani daga fadar shugaban kasa dangane da wannan ciniki.

A baya’yan Nijeriya sun bayyana bacin ransu dangane da bukatar sayen sabon jirgin da Tinubu ya yi.

MASU ALAKA

Jirgin
Labarai

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Jirgin
Labarai

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Next Post
NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

NNPC Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3 A 2023

LABARAI MASU NASABA

Jirgin

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Jirgin

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Jirgin

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Jirgin

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.