• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Shugabanni: Sabon Rikici Ya Kunno Kai A PDP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan ne jam’iyyar PDP ta gudanar da zaben shugabannin a matakin kananan hukumomi, sai dai kuma zabe ya bar baya da kura wanda ya haifar da wani sabon rikici a cikin jam’iyyar PDP bayan zargin da ake yi wa mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Illiya Damagum da sakataren gudanar da zabe, Umar Bature na sauya sakamakon zaben da aka gudanar a jihohi.

 

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa, Kola Ologbondiyan, wanda kuma ya caccaki Damagum da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, kan rubuta wa kotun daukaka kara da ke Jihar Ribas cewa jam’iyyar za ta ci gaba da daukaka kara kan ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas 27 da suka sauya sheka, sabanin matakin da aka dauka kan mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a Mista Ajibade.

  • Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar
  • Kudirin Wa’adin Shekaru 6 Ga Shugaban Kasa Ya Tsallake Karatu Na Farko

Tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa ya saba wa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ne ta hanyar daukar wannan mataki ba tare da bin umarnin mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa ba, wanda a cewarsa sashi na 42 (1) ya bai wa jam’iyyar damar zabar wakili kan harkokin shari’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

Ologbondiyan ya yi kira ga sauran mambobin kwamitin ayyuka na kasa wadanda ba su goyi bayan matakin da Damagum ya dauka ba, su kira taron gaggawa na kwamitin gudanarwar domin kada kuri’ar rashin amincewa da shugaban riko na kasa da kuma sakataren jam’iyyar na kasa.

 

Karar mai lamba PHC/2177/CS/2024, ta ta’allaka ne kan takaddamar sauya sheka da ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas su 27 suka yi zuwa jam’iyyar APC a ranar 11 ga Disamba, 2023.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a kwanakin baya ne jam’iyyar PDP ta gudanar da taronta na mazabu da na kananan hukumomi. Babban taron a wasu jihohin kamar Kogi da Binuwai, Katsina ya haifar da zazzafar muhawara a tsakanin shugabannin jam’iyyar a jihohin.

 

Sai dai da yake tattaunawa a gidan talabijin na Arise, yayin da yake mayar da martani kan lamarin Jihar Ribas, Ologbondiyan ya ce, “Lokacin da na fara ganin waccan wasikar, ban yarda ba, amma ba zato ba tsammani shugaban rikon jam’iyyar na kasa da kuma sakatarenmu na kasa sun rubuta wasika wanda ya saba wa sashe na 42 (1) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar, wanda ya ba da ikon zabar wakili na bangaren shari’a ga duk wani lamarin da ya shafi shari’a na kasa kan mai ba da shawara a harkokin shari’a na kasa.

 

“Cewa mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Illiya Damagum da Sanata Anyanwu za su gabatar da wata takarda zuwa kotun daukaka kara, ban yarda ba. Amma cikin sa’o’i 24 na tabbatar da hakan, wannan wani irin babban abin kunya ne?

 

“A wannan hali ne muka samu jam’iyyarmu. Kuma ban ma ga wani abin mamaki ba, musamman a Jihar Benuwai a jam’iyyarmu, Cif Sesgu Angba yana fitowa ya ba da labarin abubuwan da ke faruwa a kusan kowace jiha ta tarayya, inda aka yi kokarin murde zaben shugabannin a matakin kananan hukumomi, wanda ake zargin sakataren shirya taron, Bature da Damagum da Sanata Anyanwu suna aikatawa.

 

“Ban fahimci abin da ake nufi da manufar wannan duka ba, amma wannan abin damuwa ne. Kuma tun jiya shugabannin jam’iyyar suka yi ta kira da tattaunawa a tsakanin juna suna tambaya cewa, “Wannan shi ne karshe? Wannan ne irin shugabanci da muka tsinci kanmu a ciki?

 

“Na sha fada a baya cewa abun kunya ne mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa ya gurfana a gaban kwamitin gudanarwa da kwamitin zartarwa da kuma kwamitin amintattun jam’iyya kan saba wat sarin mulkin jam’iyyar PDP.

“Don haka zai gurfana a gaban kotu ne kan dukkan sassan jam’iyyar, saboda kawai yana son ya zauna a kan mukaminsa ko ta halin ya ya,” in ji shi.

A cewar Ologbondiyan, akwai shirin ruguza jam’iyyar, lamarin da ke faruwa a Jihar Ribas, wanda ya nuna cewa mukaddashin shugaban jam’iyyar yana tare da ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.

Ologbondiyan ya kuma zargin Damagum da sauya jadawalin gudanar da zaben ba tare da izini ba, wanda ya tsawaita gudanar da taron kwamitin gudanarwa har zuwa watan Satumba.

A karshen makon da ya gabata ne, ‘yan majalisar tarayya na jam’iyyar adawa suka zargi Damagum da Anyanwu da shirya makarkashiyar dagula muradun jam’iyyar PDP a Jihar Ribas.

‘Yan majalisar karkashin jagorancin Hon. Ikenga Ugochinyere, sun ce Damagun da Anyawu sun nuna adawa da matakin da PDP ta dauka na mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa na ganin an kawar da ‘yan majalisar da ke goyon bayan Wike da suka koma jam’iyyar APC tare da hana su cutar da muradun PDP da kuma yiwuwar tsige Gwamna Siminalayi Fubara a matsayin gwamnan Ribas.

Ugochinyere ya bayyana cewa, babbar kotun Jihar Ribas ta bayar da umarni a ranar 8 ga watan Yuli, 2024, inda ta hana manyan jami’an jihar yin mu’amala da ‘yan majalisar da suka sauya sheka.

Sai dai ya yi zargin Dakta J.Y. Musa, na shigar da kara kan wannan umarni, duk da adawar da mai bai wa PDP shawara kan harkokin shari’a ya nuna.

Ya ce, “Mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a na kasa, wanda tsarin jam’iyyar ya ba shi ikon kare muradun jam’iyyar PDP, ya riga ya janye karar a ranar 24 ga Yuli, 2024, bisa la’akari da irin illar da zai iya yi wa jam’iyyar.

“A wani lamari mai ban mamaki da ya faru a ranar 15 ga Agusta, 2024, Damagum da Anyanwu sun aika da wasika zuwa kotun daukaka kara da ke Fatakwal, inda suka nesanta kansu da hukuncin kotu, tare da yin zagon kasa ga matakin da mai ba da shawara kan harkokin shari’a ya dauka,” in ji Ugochinyere.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

Next Post

Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

Related

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

5 days ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

5 days ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

4 weeks ago
PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

4 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

4 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

1 month ago
Next Post
Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.