ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Shugabanni: Sabon Rikici Ya Kunno Kai A PDP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
PDP

A kwanakin nan ne jam’iyyar PDP ta gudanar da zaben shugabannin a matakin kananan hukumomi, sai dai kuma zabe ya bar baya da kura wanda ya haifar da wani sabon rikici a cikin jam’iyyar PDP bayan zargin da ake yi wa mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Illiya Damagum da sakataren gudanar da zabe, Umar Bature na sauya sakamakon zaben da aka gudanar a jihohi.

 

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa, Kola Ologbondiyan, wanda kuma ya caccaki Damagum da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, kan rubuta wa kotun daukaka kara da ke Jihar Ribas cewa jam’iyyar za ta ci gaba da daukaka kara kan ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas 27 da suka sauya sheka, sabanin matakin da aka dauka kan mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a Mista Ajibade.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar
  • Kudirin Wa’adin Shekaru 6 Ga Shugaban Kasa Ya Tsallake Karatu Na Farko

Tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa ya saba wa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ne ta hanyar daukar wannan mataki ba tare da bin umarnin mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa ba, wanda a cewarsa sashi na 42 (1) ya bai wa jam’iyyar damar zabar wakili kan harkokin shari’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ologbondiyan ya yi kira ga sauran mambobin kwamitin ayyuka na kasa wadanda ba su goyi bayan matakin da Damagum ya dauka ba, su kira taron gaggawa na kwamitin gudanarwar domin kada kuri’ar rashin amincewa da shugaban riko na kasa da kuma sakataren jam’iyyar na kasa.

 

Karar mai lamba PHC/2177/CS/2024, ta ta’allaka ne kan takaddamar sauya sheka da ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas su 27 suka yi zuwa jam’iyyar APC a ranar 11 ga Disamba, 2023.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a kwanakin baya ne jam’iyyar PDP ta gudanar da taronta na mazabu da na kananan hukumomi. Babban taron a wasu jihohin kamar Kogi da Binuwai, Katsina ya haifar da zazzafar muhawara a tsakanin shugabannin jam’iyyar a jihohin.

 

Sai dai da yake tattaunawa a gidan talabijin na Arise, yayin da yake mayar da martani kan lamarin Jihar Ribas, Ologbondiyan ya ce, “Lokacin da na fara ganin waccan wasikar, ban yarda ba, amma ba zato ba tsammani shugaban rikon jam’iyyar na kasa da kuma sakatarenmu na kasa sun rubuta wasika wanda ya saba wa sashe na 42 (1) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar, wanda ya ba da ikon zabar wakili na bangaren shari’a ga duk wani lamarin da ya shafi shari’a na kasa kan mai ba da shawara a harkokin shari’a na kasa.

 

“Cewa mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Illiya Damagum da Sanata Anyanwu za su gabatar da wata takarda zuwa kotun daukaka kara, ban yarda ba. Amma cikin sa’o’i 24 na tabbatar da hakan, wannan wani irin babban abin kunya ne?

 

“A wannan hali ne muka samu jam’iyyarmu. Kuma ban ma ga wani abin mamaki ba, musamman a Jihar Benuwai a jam’iyyarmu, Cif Sesgu Angba yana fitowa ya ba da labarin abubuwan da ke faruwa a kusan kowace jiha ta tarayya, inda aka yi kokarin murde zaben shugabannin a matakin kananan hukumomi, wanda ake zargin sakataren shirya taron, Bature da Damagum da Sanata Anyanwu suna aikatawa.

 

“Ban fahimci abin da ake nufi da manufar wannan duka ba, amma wannan abin damuwa ne. Kuma tun jiya shugabannin jam’iyyar suka yi ta kira da tattaunawa a tsakanin juna suna tambaya cewa, “Wannan shi ne karshe? Wannan ne irin shugabanci da muka tsinci kanmu a ciki?

 

“Na sha fada a baya cewa abun kunya ne mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa ya gurfana a gaban kwamitin gudanarwa da kwamitin zartarwa da kuma kwamitin amintattun jam’iyya kan saba wat sarin mulkin jam’iyyar PDP.

“Don haka zai gurfana a gaban kotu ne kan dukkan sassan jam’iyyar, saboda kawai yana son ya zauna a kan mukaminsa ko ta halin ya ya,” in ji shi.

A cewar Ologbondiyan, akwai shirin ruguza jam’iyyar, lamarin da ke faruwa a Jihar Ribas, wanda ya nuna cewa mukaddashin shugaban jam’iyyar yana tare da ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.

Ologbondiyan ya kuma zargin Damagum da sauya jadawalin gudanar da zaben ba tare da izini ba, wanda ya tsawaita gudanar da taron kwamitin gudanarwa har zuwa watan Satumba.

A karshen makon da ya gabata ne, ‘yan majalisar tarayya na jam’iyyar adawa suka zargi Damagum da Anyanwu da shirya makarkashiyar dagula muradun jam’iyyar PDP a Jihar Ribas.

‘Yan majalisar karkashin jagorancin Hon. Ikenga Ugochinyere, sun ce Damagun da Anyawu sun nuna adawa da matakin da PDP ta dauka na mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa na ganin an kawar da ‘yan majalisar da ke goyon bayan Wike da suka koma jam’iyyar APC tare da hana su cutar da muradun PDP da kuma yiwuwar tsige Gwamna Siminalayi Fubara a matsayin gwamnan Ribas.

Ugochinyere ya bayyana cewa, babbar kotun Jihar Ribas ta bayar da umarni a ranar 8 ga watan Yuli, 2024, inda ta hana manyan jami’an jihar yin mu’amala da ‘yan majalisar da suka sauya sheka.

Sai dai ya yi zargin Dakta J.Y. Musa, na shigar da kara kan wannan umarni, duk da adawar da mai bai wa PDP shawara kan harkokin shari’a ya nuna.

Ya ce, “Mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a na kasa, wanda tsarin jam’iyyar ya ba shi ikon kare muradun jam’iyyar PDP, ya riga ya janye karar a ranar 24 ga Yuli, 2024, bisa la’akari da irin illar da zai iya yi wa jam’iyyar.

“A wani lamari mai ban mamaki da ya faru a ranar 15 ga Agusta, 2024, Damagum da Anyanwu sun aika da wasika zuwa kotun daukaka kara da ke Fatakwal, inda suka nesanta kansu da hukuncin kotu, tare da yin zagon kasa ga matakin da mai ba da shawara kan harkokin shari’a ya dauka,” in ji Ugochinyere.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.