• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Yanzu ba mu damuwa da ruwan sha da lantarki, muna godiya ga aminanmu Sinawa wadanda suka taimaka mana wajen gina tashoshin samar da wutar lantarki da kafa fitilu da haka rijiyoyi.” Shugaban kauyen Koniobla, malam Jean Doumbia ne ya fadi haka cikin farin ciki, lokacin da ya ga sabbin fitilu na haskaka titi da ma hasumiyar samar da ruwa da aka gina a kauyen. 

 

Kasar Mali ta dade tana fama da matsalar karancin wutar lantarki, inda kauyukanta da suka samu damar yin amfani da lantarki bai kai kaso 20% ba. Kauyen Koniobla yana kudu maso gabashin birnin Bamako, kuma kusan ba a samun lantarki a kauyen, inda mazauna kauyen su kan shiga dogon layi don su debo ruwa daga wasu rijiyoyi da ke cikn kauyen. Amma hakan ya sauya bayan da kamfanin kasar Sin ya kammala shirin samar da wutar lantarki da zafin rana a wasu kauyuka biyu da suka hada da Koniobla da Karan na kasar ta Mali a bara, inda aka kafa tsarin samar da wuta da zafin rana da ma tsarin fitilun titi da tsarin samar da ruwan famfo da zafin rana da sauransu, wadanda suka amfani al’ummar wurin sama da su dubu 10.

  • Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?
  • Xi: Sin Da Afirka Sun Zamo Sassa Na Farko Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Daga nan, ko da an shiga duhun dare, ana samun hasken fitilu a kauyukan, kuma ko yaushe ana iya samun ruwa mai tsabta da famfo da ke aiki da lantarki, har ma karin magidanta na kauyen suka sayi talabijin.

 

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Kamar yadda Mali take, matsalar karancin makamashi na yi wa bunkasuwar akasarin sassan Afirka tarnaki. Duk da haka, Allah ya albarkaci Afirka da makamashi masu tsabta, irinsu makamashin iska da na rana, wanda hakan ya samar da dama ta warware matsalar. Abin da ya faru a kauyen Koniobla, ya shaida yadda Sin da kasashen Afirka suke hadin gwiwa da juna a wannan fanni tare da haifar da nasara.

 

A hakika, bisa tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da ma shawarar ziri daya da hanya daya, kasar Sin ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye na samar da makamashi masu tsabta a kasashen Afirka. Misali a Nijeriya, tashar ruwa ta samar da wuta ta Zungeru da kamfanin kasar Sin ya gina ya kasance irinta mafi girma a kasar, wanda ke samar da lantarki da zai iya biyan bukatun birane masu girman Abuja guda biyu, sai kuma a bara, aka kaddamar da motocin safa masu aiki da lantarki na farko da kamfanin kasar Sin ya kera a birnin Lagos…

 

Kasancewar dukkansu kasashe masu tasowa, kasar Sin ta san tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba hanya ce daya tilo da za ta daidaita matsalar sauyin yanayi, da kuma tabbatar da dauwamammen ci gaba, haka kuma ta san yadda kasashen Afirka ke matukar fatan ganin samun bunkasuwarsu, da ma kalubalen da suke fuskanta, don haka take son raba nasarorin da ta cimma a fannin tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

Yanzu haka taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na gudana a birnin Beijing, kuma batun tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba na daya daga cikin batutuwan da suka fi daukar hankalin mahalarta taron. Muna da imani kan cewa, Sin da kasashen Afirka za su tsara sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa a wannan fanni, don tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen Afirka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

UNECA: Sin Na Tallafawa Afirka Sauyi Zuwa Makamashi Mai Tsabta Ta Hanyar Shigar Da EV

Next Post

An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

16 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

2 days ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

3 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

1 week ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Next Post
An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.