• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

“Yanzu ba mu damuwa da ruwan sha da lantarki, muna godiya ga aminanmu Sinawa wadanda suka taimaka mana wajen gina tashoshin samar da wutar lantarki da kafa fitilu da haka rijiyoyi.” Shugaban kauyen Koniobla, malam Jean Doumbia ne ya fadi haka cikin farin ciki, lokacin da ya ga sabbin fitilu na haskaka titi da ma hasumiyar samar da ruwa da aka gina a kauyen. 

 

Kasar Mali ta dade tana fama da matsalar karancin wutar lantarki, inda kauyukanta da suka samu damar yin amfani da lantarki bai kai kaso 20% ba. Kauyen Koniobla yana kudu maso gabashin birnin Bamako, kuma kusan ba a samun lantarki a kauyen, inda mazauna kauyen su kan shiga dogon layi don su debo ruwa daga wasu rijiyoyi da ke cikn kauyen. Amma hakan ya sauya bayan da kamfanin kasar Sin ya kammala shirin samar da wutar lantarki da zafin rana a wasu kauyuka biyu da suka hada da Koniobla da Karan na kasar ta Mali a bara, inda aka kafa tsarin samar da wuta da zafin rana da ma tsarin fitilun titi da tsarin samar da ruwan famfo da zafin rana da sauransu, wadanda suka amfani al’ummar wurin sama da su dubu 10.

  • Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?
  • Xi: Sin Da Afirka Sun Zamo Sassa Na Farko Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Daga nan, ko da an shiga duhun dare, ana samun hasken fitilu a kauyukan, kuma ko yaushe ana iya samun ruwa mai tsabta da famfo da ke aiki da lantarki, har ma karin magidanta na kauyen suka sayi talabijin.

 

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

Kamar yadda Mali take, matsalar karancin makamashi na yi wa bunkasuwar akasarin sassan Afirka tarnaki. Duk da haka, Allah ya albarkaci Afirka da makamashi masu tsabta, irinsu makamashin iska da na rana, wanda hakan ya samar da dama ta warware matsalar. Abin da ya faru a kauyen Koniobla, ya shaida yadda Sin da kasashen Afirka suke hadin gwiwa da juna a wannan fanni tare da haifar da nasara.

 

A hakika, bisa tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da ma shawarar ziri daya da hanya daya, kasar Sin ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye na samar da makamashi masu tsabta a kasashen Afirka. Misali a Nijeriya, tashar ruwa ta samar da wuta ta Zungeru da kamfanin kasar Sin ya gina ya kasance irinta mafi girma a kasar, wanda ke samar da lantarki da zai iya biyan bukatun birane masu girman Abuja guda biyu, sai kuma a bara, aka kaddamar da motocin safa masu aiki da lantarki na farko da kamfanin kasar Sin ya kera a birnin Lagos…

 

Kasancewar dukkansu kasashe masu tasowa, kasar Sin ta san tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba hanya ce daya tilo da za ta daidaita matsalar sauyin yanayi, da kuma tabbatar da dauwamammen ci gaba, haka kuma ta san yadda kasashen Afirka ke matukar fatan ganin samun bunkasuwarsu, da ma kalubalen da suke fuskanta, don haka take son raba nasarorin da ta cimma a fannin tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

Yanzu haka taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na gudana a birnin Beijing, kuma batun tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba na daya daga cikin batutuwan da suka fi daukar hankalin mahalarta taron. Muna da imani kan cewa, Sin da kasashen Afirka za su tsara sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa a wannan fanni, don tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen Afirka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Next Post
An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.