• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Bikin Cika Shekara 20 Na Sarautar Sarkin Doma A Nasarawa

by Zubairu M Lawal
1 year ago
Bikin

A ranar Asabar da ta gabata ce, Sarkin Doma, Alhaji Ahmadu Aliyu Oga Onawo ya yi bikin cika shekaru 20 bisa karagar Sarautar Doma a Jihar Nasarawa.

Taron shi ne karo na farko a tarihin Masarautar Doma, wanda manyan baki daga sassa daban-daban a fadin kasan nan suka samu hakarta. An gudanar da taron a filin makarantar firamare da ke cikin garin Doma.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Ya Taya Tebboune Murnar Sake Zama Shugaban Algeria

Manyan sarakuna da suka hada da Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar da Etso Nupe, Alhaji Yahaya Abubakar, shugaban majalisan sarakunan Jihar Taraba Aku-Uka na Wukari, Dakta Manu Ishiyaku Ada Ali da kuma manyan sarakuna da dama daga Arewa da Kudancin Nijeriya sun halarci garin Doma domin taya murna ga Sarkin Doma.

Dukkan Sarakuna Jihar Nasarawa karkashin jagorancin shugaban majalisan sarakuna jihar, Mai Shari’a Sidi Bage Muhammad Sarkin Lafia su ma sun kasance a wannan wuri. Taron ya samu halartan jami’an gwamnati daga matakin tarayya zuwa jihohi.

An gudanar da kade-kade da raye-raye na al’adun gargajiya na kabilun Kwararafa a wurin taron, makada da mawaka na gargajiya da makadan fada daban-daban sun nishadantar a filin taron.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Dukkan Kabun da ke zaune a garin Doma cikin ado da kwalliya suka halarci wajen taron. Mahaya dawakai ba a barsu a bayaba. Kade-kade da raye-raye sai wanda idanunka ya kai ko kunne ya jiyo maka.

Masu jawabi sun bayyana Sarkin Doma, Alhaji Ahmadu Aliyu Oga Onawo a matsayin Sarkin da ya cancanta a yaba masa wajen tabbatar da zaman lafiyan al’umman Doma. Sun bayyana cewa kafin hawansa kujerar Sarautar Doma, akwai rashin jituwa tsakanin al’ummomi da ke rayuwa a yankin Doma, amma tun da ya zama Sarkin Doma babu dare babu rana sai da ya tabbatar ya hada kan dukkan kabilun da ba su jituwa da juna, wanda ya samar da zaman lafiya da kaunar juna tsakanin manoma da makiyaya.

A cewarsu, ya hada kan dukkan kabilun suna mu’amala tare har ma da auratayya, wanda babu bambanci na rikicin addini a tsakanin kauye ka za da kauye kaza.

Lallai Sarkin Doma ya samu kyakyawar shaida daga ‘yan’uwansa sarakuna na Jihar Nasarawa da ma Nijeriya gaba daya. Sannan kuma ya samu kyakyawar shaida daga Gwamnatin Jihar Nasarawa da ‘yan majalisar dokokin jihar.

Malam Muhammad Ogoshi ya ce Sarkin Doma yana burgeshi, saboda baya raina duk mutimin da ya zo wajenshi. Ya ce duk abin da ya faru a gari ko kauye idan ya samu labari zai je wajen.

Itan Hasana Abubakar ta yaba da yadda sarkin ya kawo ci gaba a garin na Doma.

Sadiya Ogoshi ta ce zaman lafiyan Doma ya tabbata ne ta dalilin hadin kai da sarkin ya kawo. Ta ce yanzu baki daga Arewa sun shiga Doma suna gina gidaje suna aure suna aurar da yaransu a Doma.

Rubkat Emmanuel ta ce, “Mu a Doma sai dai mu gode wa Allah, saboda sarkinmu ya yi wa mutanin Doma komai.”

Ta roki Sarkin Doma da ya shawarci gwamnati ta kawo banki, domin garin Doma yana samun ‘yan kasuwa masu sayan agushi da ridi da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Next Post
Matatar Man Dangote: Za Mu Shigo Da Mai Idan Kudin Sufurinsa Ya Fi Sauki Daga Waje -IPMAN

Matatar Man Dangote: Za Mu Shigo Da Mai Idan Kudin Sufurinsa Ya Fi Sauki Daga Waje -IPMAN

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.