• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Bikin Cika Shekara 20 Na Sarautar Sarkin Doma A Nasarawa

by Zubairu M Lawal
10 months ago
in Labarai
0
Yadda Aka Yi Bikin Cika Shekara 20 Na Sarautar Sarkin Doma A Nasarawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar da ta gabata ce, Sarkin Doma, Alhaji Ahmadu Aliyu Oga Onawo ya yi bikin cika shekaru 20 bisa karagar Sarautar Doma a Jihar Nasarawa.

Taron shi ne karo na farko a tarihin Masarautar Doma, wanda manyan baki daga sassa daban-daban a fadin kasan nan suka samu hakarta. An gudanar da taron a filin makarantar firamare da ke cikin garin Doma.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Ya Taya Tebboune Murnar Sake Zama Shugaban Algeria

Manyan sarakuna da suka hada da Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar da Etso Nupe, Alhaji Yahaya Abubakar, shugaban majalisan sarakunan Jihar Taraba Aku-Uka na Wukari, Dakta Manu Ishiyaku Ada Ali da kuma manyan sarakuna da dama daga Arewa da Kudancin Nijeriya sun halarci garin Doma domin taya murna ga Sarkin Doma.

Dukkan Sarakuna Jihar Nasarawa karkashin jagorancin shugaban majalisan sarakuna jihar, Mai Shari’a Sidi Bage Muhammad Sarkin Lafia su ma sun kasance a wannan wuri. Taron ya samu halartan jami’an gwamnati daga matakin tarayya zuwa jihohi.

An gudanar da kade-kade da raye-raye na al’adun gargajiya na kabilun Kwararafa a wurin taron, makada da mawaka na gargajiya da makadan fada daban-daban sun nishadantar a filin taron.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Dukkan Kabun da ke zaune a garin Doma cikin ado da kwalliya suka halarci wajen taron. Mahaya dawakai ba a barsu a bayaba. Kade-kade da raye-raye sai wanda idanunka ya kai ko kunne ya jiyo maka.

Masu jawabi sun bayyana Sarkin Doma, Alhaji Ahmadu Aliyu Oga Onawo a matsayin Sarkin da ya cancanta a yaba masa wajen tabbatar da zaman lafiyan al’umman Doma. Sun bayyana cewa kafin hawansa kujerar Sarautar Doma, akwai rashin jituwa tsakanin al’ummomi da ke rayuwa a yankin Doma, amma tun da ya zama Sarkin Doma babu dare babu rana sai da ya tabbatar ya hada kan dukkan kabilun da ba su jituwa da juna, wanda ya samar da zaman lafiya da kaunar juna tsakanin manoma da makiyaya.

A cewarsu, ya hada kan dukkan kabilun suna mu’amala tare har ma da auratayya, wanda babu bambanci na rikicin addini a tsakanin kauye ka za da kauye kaza.

Lallai Sarkin Doma ya samu kyakyawar shaida daga ‘yan’uwansa sarakuna na Jihar Nasarawa da ma Nijeriya gaba daya. Sannan kuma ya samu kyakyawar shaida daga Gwamnatin Jihar Nasarawa da ‘yan majalisar dokokin jihar.

Malam Muhammad Ogoshi ya ce Sarkin Doma yana burgeshi, saboda baya raina duk mutimin da ya zo wajenshi. Ya ce duk abin da ya faru a gari ko kauye idan ya samu labari zai je wajen.

Itan Hasana Abubakar ta yaba da yadda sarkin ya kawo ci gaba a garin na Doma.

Sadiya Ogoshi ta ce zaman lafiyan Doma ya tabbata ne ta dalilin hadin kai da sarkin ya kawo. Ta ce yanzu baki daga Arewa sun shiga Doma suna gina gidaje suna aure suna aurar da yaransu a Doma.

Rubkat Emmanuel ta ce, “Mu a Doma sai dai mu gode wa Allah, saboda sarkinmu ya yi wa mutanin Doma komai.”

Ta roki Sarkin Doma da ya shawarci gwamnati ta kawo banki, domin garin Doma yana samun ‘yan kasuwa masu sayan agushi da ridi da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BikiNasarawaSarkin Doma
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Matatar Man Dangote: Za Mu Shigo Da Mai Idan Kudin Sufurinsa Ya Fi Sauki Daga Waje -IPMAN

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

2 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

5 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

11 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

12 hours ago
Next Post
Matatar Man Dangote: Za Mu Shigo Da Mai Idan Kudin Sufurinsa Ya Fi Sauki Daga Waje -IPMAN

Matatar Man Dangote: Za Mu Shigo Da Mai Idan Kudin Sufurinsa Ya Fi Sauki Daga Waje -IPMAN

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.