• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

by Khalid Idris Doya
9 months ago
in Rahotonni
0
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Arewacin Nijeriya, musamman arewa maso yamma na fama da matsanancin kalubalen tsaro na garkuwa da mutane da kashe-kashe sakamakon barnar ‘yan bindiga ko kuma ‘yan fashin daji kamar yadda wasu ke kiran su a yanzu. 

Matsalar ‘yan fashin daji dai ta fara kunno kai gadan-gadan ce a shekarar 2011, biyo bayan rikice-rikicen manoma da makiyaya da aka fara samu a arewa maso yammacin Nijeriya. ‘Yan fashin daji a jihohin Zamfara, Kaduna, Katsina sun zama babban barazana ga zaman lafiya a ‘yan shekarun baya. Sun addabi kauyuka da daman gaske.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Asibitin Gombe Ya Haramtawa Ma’aikata Yin Kiripto Lokacin Aiki

Zuwa yanzu, hukumomin tsaro na ci gaba da kokarinsu na kawo karshen masu garkuwa da mutane a arewa. Lamarin da ake samun nasarori duk da cewa a wasu lokutan su ma sojoji na rasa rayukansu a kokarinsu na dakile ‘yan ta’addan.

Jiragen yakin sojojin kasar sun kaddamar da hare-hare daban-daban kan maboyar ‘yan bindigan kuma an samu nasarorin sosai.

A watan Mayu, ministan tsaro Muhammadu Badaru Abubakar ya ce ta hanyar hadin guiwar aiki tsakanin shugabannin hukumomin tsaro da takwarorinsu an samu nasarar kashe ‘yan fashin daji da ‘yan ta’adda sama da 9,300, yayin da aka cafke wasu 7,000 tun a shekarar da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A baya-bayan nan, rundunar sojin Nigeriya ta kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan fashin daji kuma mai sarrafa makamai Kachalla Halilu Sububu, a cikin samamen da suke kaddamarwa kan ‘yan fashin daji a arewa maso yamma.

Sububu, wani jigo ne a harkokin fashi da makami kuma ya mallaki wani katafaren wurin hakar ma’adinai a Dan-Kamfani da ke karamar hukumar Anka, sannan ya mallaki dubban shanu a dajin Sububu.

Kazalika, wasu ‘yan fashin daji da dama ne sojoji suka ayyana nemansu ruwa a kallo bisa shiga harkokin da suka shafi ta’addanci. Jerin kasurguman ‘yan fashin daji da sojoji suka halaka sun hada da

Halilu Sububu da Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da “Buharin Yadi”, gawurtaccen dan ta’adda ne da ya addabi jama’a a Kidandan/Galadimawa da ke karamar hukumar Giwa, Sabon Birni da Kerawa a karamar hukumar Igabi da wasu sassa da dama da suke iyaka da karamar hukumar Sabuwa ta Jihar Katsina da kuma wasu sassan Jihar Neja da Zamfara.

Akwai kuma wani shugaban ‘yan garkuwa da mutane da ake kira da Dangote ya bakwancin lahira a wani artabun da suka fafata da sojoji a sansani Kachalla Dankarami da ke kusa da dajin Dumbunrun a tsakanin Batsari da karamar hukumar Jibiya na Jihar Katsina.

Boderi Isyaku, fitaccen shugaban masu sace mutane don neman kudin fansa, wanda ya jagoranci garkuwa da daliban kwalejin neman dazuka su 39. Kuma shi ne ya shirya kai hari a kwalejin horas da sojoji ta NDA da ke Kaduna a 2021, wanda shi ya bakonci lahira.

Sannan akwai Kachalla Dan Chaki da Dogo Gudali da Dogo Rabe, wanda aka kashe shi ne wani harin da sojojin suka kai a ci gaba da share ‘yan fashin daji da suka addabi al’ummar Zurmi da Birnin Magaji a Jihar Zamfara da kuma yankin Jibiya a Jihar Katsina.

Alhaji Auta da Kachalla Ruga dukkaninsu sun bakwancin lahira tare da wasu mambobin tawagar a lokacin da aka yi ram da su a dajin Gusami da kauyen Tsamre a karamar hukumar Birnin Magaji ta Jihar Zamfara.

Rufai Maikaji, shi kuma kusa ne da ya jagoranci kashe mutane da dama a harkokin garkuwa da mutane. Shi ma ya bakwancin lahira.

Ya’u, an kashe shi a wani kwantan bauna da sojoji suka kai musu a dajin Burra da ke karamar hukumar Ningi a Jihar Bauchi. Shi din shugaban gungun ‘yan fashin daji ne masu dauke da muggan makamai da suka addabi jama’a a Burra da makwabtanta da garkuwa da mutane da kuma kashe-kashe.

Alhaji Karki, shi ma ya mutu a lokacin da ya yi arangama da sojoji a Jihar Neja. Karki, wanda ya yi tirjiya daga baya sojojin sun sha karfinsa, shi addabi al’umman Neja da ta’addanci kama daga garkuwa da mutane da neman kudin fansa da sauransu.

Shugaban ‘yan fashin daji “Yellow” ya jagoranci masu garkuwa a sansanin daban-daban da suke Zamfara, Kaduna, da Katsina, ya bakwancin lahira bayan da sojojin suka yi luguden wuta a jihohin Katsina da Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaTa'addanciYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Next Post

Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Ƙasurguman
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.