• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

by Khalid Idris Doya
12 months ago
in Rahotonni
0
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Arewacin Nijeriya, musamman arewa maso yamma na fama da matsanancin kalubalen tsaro na garkuwa da mutane da kashe-kashe sakamakon barnar ‘yan bindiga ko kuma ‘yan fashin daji kamar yadda wasu ke kiran su a yanzu. 

Matsalar ‘yan fashin daji dai ta fara kunno kai gadan-gadan ce a shekarar 2011, biyo bayan rikice-rikicen manoma da makiyaya da aka fara samu a arewa maso yammacin Nijeriya. ‘Yan fashin daji a jihohin Zamfara, Kaduna, Katsina sun zama babban barazana ga zaman lafiya a ‘yan shekarun baya. Sun addabi kauyuka da daman gaske.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Asibitin Gombe Ya Haramtawa Ma’aikata Yin Kiripto Lokacin Aiki

Zuwa yanzu, hukumomin tsaro na ci gaba da kokarinsu na kawo karshen masu garkuwa da mutane a arewa. Lamarin da ake samun nasarori duk da cewa a wasu lokutan su ma sojoji na rasa rayukansu a kokarinsu na dakile ‘yan ta’addan.

Jiragen yakin sojojin kasar sun kaddamar da hare-hare daban-daban kan maboyar ‘yan bindigan kuma an samu nasarorin sosai.

A watan Mayu, ministan tsaro Muhammadu Badaru Abubakar ya ce ta hanyar hadin guiwar aiki tsakanin shugabannin hukumomin tsaro da takwarorinsu an samu nasarar kashe ‘yan fashin daji da ‘yan ta’adda sama da 9,300, yayin da aka cafke wasu 7,000 tun a shekarar da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

A baya-bayan nan, rundunar sojin Nigeriya ta kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan fashin daji kuma mai sarrafa makamai Kachalla Halilu Sububu, a cikin samamen da suke kaddamarwa kan ‘yan fashin daji a arewa maso yamma.

Sububu, wani jigo ne a harkokin fashi da makami kuma ya mallaki wani katafaren wurin hakar ma’adinai a Dan-Kamfani da ke karamar hukumar Anka, sannan ya mallaki dubban shanu a dajin Sububu.

Kazalika, wasu ‘yan fashin daji da dama ne sojoji suka ayyana nemansu ruwa a kallo bisa shiga harkokin da suka shafi ta’addanci. Jerin kasurguman ‘yan fashin daji da sojoji suka halaka sun hada da

Halilu Sububu da Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da “Buharin Yadi”, gawurtaccen dan ta’adda ne da ya addabi jama’a a Kidandan/Galadimawa da ke karamar hukumar Giwa, Sabon Birni da Kerawa a karamar hukumar Igabi da wasu sassa da dama da suke iyaka da karamar hukumar Sabuwa ta Jihar Katsina da kuma wasu sassan Jihar Neja da Zamfara.

Akwai kuma wani shugaban ‘yan garkuwa da mutane da ake kira da Dangote ya bakwancin lahira a wani artabun da suka fafata da sojoji a sansani Kachalla Dankarami da ke kusa da dajin Dumbunrun a tsakanin Batsari da karamar hukumar Jibiya na Jihar Katsina.

Boderi Isyaku, fitaccen shugaban masu sace mutane don neman kudin fansa, wanda ya jagoranci garkuwa da daliban kwalejin neman dazuka su 39. Kuma shi ne ya shirya kai hari a kwalejin horas da sojoji ta NDA da ke Kaduna a 2021, wanda shi ya bakonci lahira.

Sannan akwai Kachalla Dan Chaki da Dogo Gudali da Dogo Rabe, wanda aka kashe shi ne wani harin da sojojin suka kai a ci gaba da share ‘yan fashin daji da suka addabi al’ummar Zurmi da Birnin Magaji a Jihar Zamfara da kuma yankin Jibiya a Jihar Katsina.

Alhaji Auta da Kachalla Ruga dukkaninsu sun bakwancin lahira tare da wasu mambobin tawagar a lokacin da aka yi ram da su a dajin Gusami da kauyen Tsamre a karamar hukumar Birnin Magaji ta Jihar Zamfara.

Rufai Maikaji, shi kuma kusa ne da ya jagoranci kashe mutane da dama a harkokin garkuwa da mutane. Shi ma ya bakwancin lahira.

Ya’u, an kashe shi a wani kwantan bauna da sojoji suka kai musu a dajin Burra da ke karamar hukumar Ningi a Jihar Bauchi. Shi din shugaban gungun ‘yan fashin daji ne masu dauke da muggan makamai da suka addabi jama’a a Burra da makwabtanta da garkuwa da mutane da kuma kashe-kashe.

Alhaji Karki, shi ma ya mutu a lokacin da ya yi arangama da sojoji a Jihar Neja. Karki, wanda ya yi tirjiya daga baya sojojin sun sha karfinsa, shi addabi al’umman Neja da ta’addanci kama daga garkuwa da mutane da neman kudin fansa da sauransu.

Shugaban ‘yan fashin daji “Yellow” ya jagoranci masu garkuwa a sansanin daban-daban da suke Zamfara, Kaduna, da Katsina, ya bakwancin lahira bayan da sojojin suka yi luguden wuta a jihohin Katsina da Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaTa'addanciYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Next Post

Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

Related

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

5 days ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

5 days ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

6 days ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

1 week ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 weeks ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

3 weeks ago
Next Post
Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.