• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

by Hussein Yero
1 year ago
Hatsarin

A ranar Asabar da ta gabata ne, jirgin kwale-kwale ya nitse da manoma a gwadaben bakin kasuwar da ke Karamar Hukumar Gummi ta Jihar Zamfara. 

An samu sabanin alkaluma na adadin wadanda suka rasa rayukansu; sakamakon taho mu gamu da kwale-kwalen ya yi da wani kwale-kwalen dauke da fasinjoji a ciki, wasu kafafen yada labarai sun bayyana cewa, sama da mutum 46 ne suka rasu.

  • Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou
  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

Wannan dalili ne yasa, Fadar Shugaban Kasa da Ofishin Gwamnan Jihar Zamfara, suka fitar da sanarwar jaje tare da yin ta’aziya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da sauran al’ummar Zamfara da kasa baki-daya.

Guda daga cikin fasinjojin da tsira daga hatsarin da kwale-kwalen ya yi, Abubakar Danjuma; ya shaida wa wakilinmu yadda abin ya faru da kuma yadda Allah ya tseratar da shi, inda yake cewa; “Muna cikin kwale-kwalen, bayan mun kai tsakiyar ruwa; sai ga wani kwale-kwalen daga inda muka dosa ya kunno kai kawai ya bangaji namu kwale-kwalen; inda nan take igiyarsa ta katse.

Daga nan ne kuma, sai kawai kwale-kwalen namu ya fara tangal-tangal ruwa ya fara shiga ciki, sai ya rika yin kasa ruwa na ci gaba da shiga cikin nasa. Saboda haka, kafin zuwa wani dan lokaci; mun nitse a cikin ruwa, amma cikin ikon Allah da yake wasu daga cikinmu mun iya ruwa; sai Allah ya tseratar da rayukanmu, aka kuma samu nasarar ceto wasu daga ciki. Saboda haka, muna yi wa Allah godiya da ya kubutar da mu”, in ji Danjuma.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shi kuwa, wanda ya rasa dansa; Malam Ibrahim ya bayyana cewa, haka Allah ya rubuta wa dana Muhammad cewa, a hadarin kwale-kwalen zai rasu; shi yasa ya amshi bawan nasa. Don haka, babu abin da zance da wuce Allah ya ji kansa tare da sauran wadanda suka rasu.

A nata banganen kuwa, Gwamnatin Jihar Zamfara; karkashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal, ta bai wa iyalan mamatan tallafin Naira miliyan ashirin.

Mataimakin Gwamnan Jihar, Malam Mani Mummuni ne ya bayyana haka, a lokacin ziyarar ta’aziya ga iyalan mamatan a Fadar Mai Martaba, Sarkin Mafaran Gummi, mai shari’a Hassan Lawal.

Mataimakin, ya kuma bayyana bakincikinsa ga iyalan wadanda suka rasu tare kuma da jajanta wa ‘yan’uwa da abokan arziki.

“Yanzu haka, mun bai wa kwamitin rabon tallafin agajin gaggawa wanda gwamnati ta kafa, karkashin jagorancin Alhaji Salihu mai buhu Gummi, wannan tallafi na Naira miliyan ashirin da za a raba wa iyalan wadanda iftila’in ya shafa.

“Haka zalika, gwamna yana tare da Shugabannin Hukumomin ba da agajin gaggawa da kuma hukumomin da abin ya shafa a kan matsalar madatsun ruwa, don gano matsalar da ke haifar da wadannan hadarurruka; domin kaucewa sake afkuwarsa a nan gaba,” in ji Mataimakin Gwamnan.

Haka zalika, Mataimakin Gwamnan; ya bayar da tabbacin cewa, dukkanin gwadaben da ake amfani da shi wajen tsallake ruwa, babu shakka gwamati za ta yi iya kokarinta na ganin ta samar da mafita.

Mai Martaba Sarkin Mafaran Gummi, Mai Shari’a Hassan Lawal; ya bayyana godiyarsa ga Gwamnatin Jihar Zamfara, kan ta’aziya da kuma tallafin kudi na Naira miliyan ashirin ga iyalan wadannan mamata.

Sarkin, ya kuma tabbatar da cewa; mutane goma ne kadai suka rasa rayukansu, ba arba’in ba kamar yadda wasu kafafen yada labarai suka bayyana. Kazalika, nan take ya bayyana sunayensu a gaban mahaifansu a cikin fadar tasa.

Sarkin Mafaran, ya kuma tabbatar wa da Mataimakin Gwamnan cewa; ya gayyato kungiyar masu kula da kwale-kwalen Jihar Kogi, don neman shawara a kan yadda za a magance matsalar asarar rayuka; sun kuma ba da tasu shawarar za kuma a mika zuwa ga gwamnati, domin shawo kan matsalar.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Gummi, Nuhu Falale ya bayyana cewa, kin bin doka ga shugabannin masu kulawa da kwale-kwalen, ke haifar da asarar rayukan al’umma.

A karshe, Falale ya yi kira ga gwamnatin jihar; ta taimaka wajen sama musu kwale-kwalen zamani, wanda za su rika amfani da shi wajen jigilar al’ummarsu, domin kaucewa asarar rayuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Yunƙurin Sayar Da Jariri, Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 2 A Legas

Yunƙurin Sayar Da Jariri, Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 2 A Legas

LABARAI MASU NASABA

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.