• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ndume Ya Bukaci Tinubu Ya Dauko Sojojin Haya Don Yakar ‘Yan Ta’adda

by Sadiq
12 months ago
in Labarai
0
Ndume Ya Bukaci Tinubu Ya Dauko Sojojin Haya Don Yakar ‘Yan Ta’adda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu a majalisar dattawa, Mohammed Ali Ndume, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya dauko sojojin haya don kawar ‘yan ta’addan Boko Haram a Jihar Borno.

Ndume, ya yaba da irin rawar da sojojin Nijeriya ke takawa, amma ya ce ba su da kayan aikin da za su yaki ‘yan tada kayar baya a yankin Arewa maso Gabas.

  • Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Jirgin Ruwa Dauke Da ‘Yan Maulidi 200 Ya Nutse A Neja

Ya ce manyan kasashen duniya suna daukar sojojin haya don taimaka musu a yaki da ‘yan ta’adda.

Ya ce kasashe irin su Amurka da Rasha da Birtaniya da Faransa da dai sauransu, suna amfani da sojojin haya.

Sanatan ya bayyana cewa matakin zai kasance na wucin gadi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Ndume, ya yi wannan kiran ne a kan yadda ‘yan ta’addan Boko Haram suka kashe wasu manoma shida a garin Ngoshe da ke karamar hukumar Gwoza ta Jihar Borno, tare da sace wasu biyar da suka hada da mata.

Ya koka da yadda hare-haren Boko Haram ke tilastawa manoma barin amfanin gonakinsu daidai lokacin da kasar ke fama da matsalar karancin abinci.

“A duk fadin duniya, gwamnatoci suna daukar hayar sojoji don shiga wasu wurare. Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya daukar wannan mataki na wucin gadi. Wadannan sojoji za su iya aiki da Civilian JTF kafada da kafada.

“Wadannan ‘yan kwangila za su zo da kayan aikinsu da kayan aikin soja. A cikin kankanin lokaci, za su kawar da ‘yan ta’addar Boko Haram.

“Ana kuma iya amfani da su wajen kawar da ‘yan fashin daji a Arewa maso Yamma.

“Gwamnatin Tarayya za ta iya daukar matasa aikin soja akalla miliyan daya. Hakan zai taimaka wajen yaki da ta’addanci.”

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a baya-bayan nan, ‘yan ta’addan sun kashe kwamandan Civilian JTF, Jubril Dada Zarana.

Sabon harin na zuwa ne ‘yan makonni kadan bayan da ‘yan ta’addan suka kashe mutane da dama a ta hanyar amfani da bam.

 

 

 

 

 

 

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramNdumeSojojin HayaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai

Next Post

Tinubu Zai Yi Balaguro Zuwa Birtaniya Na Mako 2

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

6 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

9 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

9 hours ago
Sojojin Haya
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

11 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

12 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

13 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Zai Yi Balaguro Zuwa Birtaniya Na Mako 2

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Sojojin Haya

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.