• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Sabon Harin Bam Na Kaduna

by Shehu Yahaya and Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Sabon Harin Bam Na Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Yadda Abin Ya Faru –Ganau
  • Tabbas ‘Yan Ta’adda Muka Farmaka –NAF

Al’ummar Kauyen Jika da Kolo da ke garin Yadin Kidandan a karamar hukumar Giwa da ke Jihar Kaduna na ci gaba da zaman dar-dar bisa zargin kai musu hari da jiragen sojin saman Nijeriya ya kai musu a makon da ya gabata.

 

Al’ummar garin sun zargi sojojin sama da jefa musu bam yayin da suke gudanar da sallar Juma’a a cikin masallaci da kuma kasuwa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 23.

  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Za Su Kaɗa Ƙuri’ar Kawo Canji Na Gaskiya A 2027 – Kwankwaso
  • Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina

Harin bam din ya haifar da cece-kuce tsakanin al’ummar garin da runduna sojin saman Nijeriya, inda mutanan kauyen suke zargin sojoji sun kai harin mai uwa da wabi.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

Sai dai a nata, bangaren rundunar sojin saman Nijeriya ta musanta wanna zargi, ta kuma bayyana cewa harin da ta kai ya tafi kai tsaye ne ga sansanin babban dan bindiga mai suna Kadade Gurgu, wanda na hannun daman dan ta’adda Dogo Gide ne.

 

A wata ziyara da wakilinmu ya kai a yankin karamar hukumar Giwa, wasu mazauna garin sun bayyana cewa akwai fararen hula da harin sojojin ya shafa.

 

Haka zalika, sun kamanta harin da sojojin suka kai da wanda aka kai a baya a garin Tudun Biri, wanda ya yi sanadiyyar rasa ran masu Mauludi kimamnin guda 100 a watan Disamban 2023.

 

Wani magidancin dan asalin garin Kidandan, ya bayyana wa wakilinmu yadda abin ya faru, yana mai cewa, “Bisa batun tsaro ba zan iya bayyana sunana ba, amma dai ni dan asalin garin Kidandan ne kuma a nan aka haife, sannan a nan nake rayuwa, bisa matsalar tsaro ya sanya muke zuwa garin jifa-jifa.

 

“Yadin Kidandan gari ne wanda ya zama sansanin ‘yan ta’adda. Wanda yanzu shiga garin idan kai ba dan gari ba ne ba ya shiguwa. Ranar Juma’ar da ta gabata, wani jirgi ya kai hari har ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Amma batun gaskiya shi ne, har yanzu babu wani wanda zai iya tantance cewa wadanda suka mutu a harin ‘yan garin ne kadai babu ‘yan ta’adda a ciki, saboda gari ne wanda yake cakude da mutanan kirki da ‘yan ta’adda.”

 

Wani mazaunin garin Jika da Kolo da ke zaune a garin Gwargwaji a Zariya ya shaida cewa, “Yawancinmu har yanzu muna zaune a kusa da kauyen, saboda ba mu da wani wurin da za mu koma. A nan aka haifi kakanninmu.

 

Mun rasa ‘yan uwanmu da yawa, ciki har da yara marasa laifi.

 

“Kuma batun cewa harin ya rusa da masallaci ba haka ba ba ne. An dai kashe mutane amma harin bai taba masallaci ba.”

 

Sai dai wani bincike da LEADERSHIP HAUSA ta gudanar ya nuna cewa masallacin da al’ummar garin na Jika da Kolo suke zargin sajojin sun kai hari, dan siyasa daga Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali Amin “Little”, ya gina musu. Wanda yake kusa da wat babbar gonarsa da ke yankin domin gudanar da sallar Juma’a.

 

Majiyarmu ta shaida mana cewa shekaru biyu baya, shi kansa dan siyasar ya tsallake rijiya da baya daga hannun ‘yan ta’adda, inda aka harbe shi a hannu, lamarin da sanya ya dakatar da zuwa gonar bisa matsalar rashin tsaro.

 

A wata sanarwar da rundunar sojan sama ta fitar ta hannun daraktan yada labaranta, Kaftin Kabiru Ali, ya jaddada cewa ba su Kai hari a masallaci ba, kuma duk wani bayani zai zo ne bayan da rundunar ta kammala bincike.

 

Rundunar ta kara da cewa ta kashe ‘yan ta’adda da dama yayin harin da ta kai, amma babu masallaci a wurin da jiragen suka kai harin.

 

A wata zantawa da ya yi da wakilinmu, Kansilar Mazabar Kidandan, Abdullahi Ismail, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce kauyen Jika da Kolo ya zama sansanin ‘yan ta’adda da suke cin kasuwarsu babu babbaka.

 

Majiyarmu ta tabbatar da cewa an yi jana’izar mutane da suka ransu su 23.

 

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin kwamshinan harkokin tsaro na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan kan lamarin, inda ya kira wayarsa har sau uku bai dauka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'ummar Tudun BiriHarin sojoji ga yan gariNAF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Za Su Kaɗa Ƙuri’ar Kawo Canji Na Gaskiya A 2027 – Kwankwaso

Next Post

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Related

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

5 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

9 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

10 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

24 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

1 day ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

1 day ago
Next Post
NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.