• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Bunkasuwar Sin Bisa Yadda Aka Fitar Da Al’ummar Jino Daga Kangin Talauci

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Nazari Kan Bunkasuwar Sin Bisa Yadda Aka Fitar Da Al’ummar Jino Daga Kangin Talauci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, na kai ziyara kauyen Bapo, kauye ne na al’ummar kabilar Jino da da ke yankin Xishuangbanna na lardin Yunnan dake kudu masu yammacin Sin, inda na ga an rataya hoton tsohon shugaban kasar Sin marigayi Mao Zedong a kofar gidajen mazauna kauyen, kuma Miko wadda ke rayuwa a kauyen ta fada min cewa, dalilin hakan shi ne don bayyana godiya da amincewarsu ga gwamnatin Sin.

 

Ta ce, a watan Oktoba na shekarar 1952 bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, gwamnatin kasar Sin ta tura tawagogin aiki zuwa sassan dake fama da matukar talauci da ke karkarar lardin Yunnan. Ma’aikatan tawagogin sun yi rayuwa da aiki tare da mazauna wuri, sun yi ayyuka da suka hada da gina madatsar ruwa da gidaje, da aikin debo ruwa da daka shimkafa, kana sun taimakawa al’ummar wuri a mabambantan harkoki, wanda hakan ya sa al’ummar Jino suka fita daga zamantakewar al’umma irin ta zamanin da da can.

  • Waƙa Sana’a Ce Sai Da Ilimi Da Jari -Wizzamany
  • Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

A halin yanzu, iri wadannan tawagogi na ci gaba da aikinsu a tsaunuka dake Xishuangbanna, kuma ma’aikatan sun gaji ruhi daga tsoffinsu, suna kokarin fitar da hanyoyi mafiya dacewa na farfado da kauyuka da raya sana’o’in wurin. Har ma mazauna wuri su kan ce, yadda ba za a bar gishiri a rayuwa ba, hakan nan ma ba za a bar tawagogin ba.

 

Labarai Masu Nasaba

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

Miko ta ce, a da zaman rayuwar al’ummar Jino ya godara ne kan aikin farauta, kuma al’ummar Jino suna shuka ganyen shayi don biyan bukatunsu ne kawai. Amma daga baya gwamnatin wurin ta yi amfani da fifikon da al’ummar Jino ke da shi don kyautata zaman rayuwarsu, inda ta gabatar da tsarin “Kauye daya haja daya”, don raya tattalin arzikin wurin.

 

Misali kauyen Bapo da na ziyarta, na dogaro da al’adun ‘yan kabilar Jino masu ban sha’awa, da ma ganyen shayi na Pu’er mai inganci, abin da ya sa ya zama kauyen da ya shahara a bangaren yawon shakatawa bisa al’adunsa a Yunnan.

 

A shekarar 2019, al’ummar Jino sun fita daga kangin talauci gaba daya. Miko ta gaya min cewa, a yanzu tsoffin gidaje dake cikin tsauni sun kasance wani sashi na bayyana al’adun Jino, bayan mutanen da a baya ke rayuwa cikinsu sun kaura zuwa gidaje na zamani.

 

Daga zamantakewar al’umma irin ta zamanin da da can, zuwa samun bunkasuwa irin ta zamani, daga gidaje marasa inganci zuwa gidaje masu inganci, daga sufurin kayayyaki ta amfani da doki zuwa motoci, zaman rayuwar al’ummar Jino na samun kyautatuwa matuka. Na zauna a gida mai rataye da hoton marigayi Mao Zedong, ina dandana shayin Pu’er, ina ganin cewa, al’ummar Jino sun tabbatar da bunkasuwa cikin sauri karkashin manufar kawar da talauci da gwamnatin kasar Sin ta dauka. A halin yanzu kuma, al’ummar Jino na kokarin kama hanyar zamanintar da kan su. (Mai zane da rubuta: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Waƙa Sana’a Ce Sai Da Ilimi Da Jari -Wizzamany

Next Post

Bara-gurbin Ma’aikaci Da Hadarin Wargaza Bin Tsarin Cancanta

Related

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

19 minutes ago
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

18 hours ago
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

19 hours ago
Dan Asalin Tudun Loess
Daga Birnin Sin

Dan Asalin Tudun Loess

20 hours ago
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba
Daga Birnin Sin

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

21 hours ago
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

22 hours ago
Next Post
Bara-gurbin Ma’aikaci Da Hadarin Wargaza Bin Tsarin Cancanta

Bara-gurbin Ma’aikaci Da Hadarin Wargaza Bin Tsarin Cancanta

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

June 16, 2025
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Jigila Kai Tsaye Zuwa Sin Da Indiya

FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa

June 16, 2025
Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

June 16, 2025
Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.