ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bara-gurbin Ma’aikaci Da Hadarin Wargaza Bin Tsarin Cancanta

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Ma'aikaci

Ma’aikaci mutum ne da aka dauke shi domin hidimta wa jama’a a cikin ayyuka irin na gwamnati, kodayake ma’aikacin yana kasuwa zuwa kashi biyu, akwai ma’aikaci mai kula da kirkiro ayyuka da sa idon ganin ana aiwatar da ayyukan, akwai kuma mai hidimta wa jama’a kai-tsaye. Kodayake duka biyun danjuma ne dai da danjummai.

Galibin ma’aikatan gwamnati masu hidimta wa jama’a kai-tsaye suna fara aiki ne a matsayin ma’aikatan da ke kula da tsare-tsare saboda ka’idojin aikin gwamnati, ban taba jin ko akwai ka’idojin aikinsu daban ba, amma kuma ina da masaniya a kan ka’idojin aikin wadanda ke hidimta wa jama’a kai-tsaye. Sun hada da dokokin daukar aiki, karin girma da ladabtarwa da ake amfani da su a kan kowane ma’aikaci. Kodayke sojoji, jami’an tsaro da sauran wasu hukumomi sun zame suka kafa nasu dokokin amma ga kowane ma’aikaci mai hidimta wa jama’a, baya ga tsarin mulki ba shi da wata doka sai ta tsarin aikin gwamnati.

  • Gwamnati Ba Za Ta Ci Gaba Da Biyan Tallafin Aikin Hajji Ba – NAHCON
  • Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

Saboda haka wane ne ma’aikacin gwamnati mai hidimta wa jama’a, wanda ake nadawa ya yi aiki a cikin harkokin gwamnati tsundum kamar irin su ministoci, jakadoji, manajan daraktoci, manyan shugabannin hukumomin gwamnati, manyan daraktoci, mambobin hukumomin sojoji da jami’an tsaro da sauransu, dukkansu ana daukarsu a matsayin masu hidimta wa jama’a ne duk da cewa akwai bambanci a bangarorin da suke yin aiki.

ADVERTISEMENT

Da zarar mutane sun fahimci wannan, to za su zage damtse wajen zama ma’aikatan gwamnati masu hidimta wa jama’a amma ba hidimta wa kansu ba. Abin da ya fi bata lamurra a yau a cikin al’ummarmu shi ne samun ma’aikatan gwamnati masu hidima ga jama’a da ba su cancanta ba kamar yadda aka ambata a littafin da tsohon Ministan Abuja kuma tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasiru El-Rufai ya rubuta.

Mutum ne sahihi mai kaifin basira, yana cikin sahun su Sule Lamido, Sarki Sanusi Lamido Sanusi, tsohon Gwamnan CBN kuma Sarkin Kano, Dr. Akinwumi Adesina, Shugaban Bankin Raya Afirka, Dr. Oby Ezekwesili, Charles Soludo, Peter Obi, Dr. Obadiah Mailafiya, Farfesa Ango Abdullahi, dukkan wadannan mutane ne masu kaifin basira da suka yi shuhura. Kuma su ne ma’aikatan gwamnati da suka hidimta wa jama’a a bisa mizanina.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Idan aka duba batun da muke magana a kai na “Ma’aikacin Gwamnati Da Ya Tsinci Kansa A Aiki”, batu ne musamman na tafka muhawara a kai, yana da ma’ana daban-daban. Misali, a wurin Malam Nasiru El-Rufa’i, hakan na nufin mutane ko mutumin da ya tsinci kansa a wani mukami da bai shirya masa ba, a wurin wasu kuma, abin ya sha bamban.

Amma me ya sa? Idan aka nada mutum a wani mukami da ba shi da cikakkiyar masaniya ko kuma bai ma san aikin da aka ba shi ba kwata-kwata, to idan yana so ya nuna kishin kasa da hali nagari, sai ya ki karba, ko ya yi murabus domin bai wa wadanda suka cancanta masu kwarewa sarari su taimaka wajen ciyar da kasa gaba.

Amma shi wanda ya zama ma’aikaci bisa kaddara ba don cancanta ba, ba zai taba yin haka ba kuma ba zai nemi ilimin wannan aiki da aka ba shi ba don samun nasara. Irin su ne za ka ga suna wa mutane kamar sun fi kowa ilimi. Sai su rika zalunci da kama-karya wajen gudanar da ofisoshinsu. Maimakon su jawo kwararru da suka san aiki sai su shamakance su. Ta haka za su rika kunyata wadanda suka nada su har ta kai ga an wayi gari an kore su, duk kunya ta lullube su saboda gazawarsu. Irin wadannan ma’aikata bata gari ne a cikin gwamnati, ba su da kima da daraja, ga kauyanci da kuma yadda suke kasancewa kadangaren bakin tulu, ka ki shiga, ka ki fita.

Irin wadannan ma’aikata marasa cancanta sun fi yawa a ofisoshin gwamnati saboda ba su da gurbi a kamfanoni masu zaman kansu ko kuma kamfanonin da ke neman riba. Nan da nan ake gane su a fatattake su, shi ya sa suke zuwa su fake a ma’aikatun gwamnati saboda an kawo su ne don suna da uwa a gindn murhu da kuma sauran harkalla marasa kyau. Don haka matukar ana so kasa ta ci gaba, dole ne a rika duba cancanta da ilimi da kaifin basira. Muna da mutane a kasar nan wadanda sun yi shuhura da kwazo da kaifin basira a duniya kamar su Dr. Ngozi Okonjo- Iweala, Dr. Amina Mohammed, Dr. Oby Ezekwesili, Dr Akinwumi Adeshina, Dr. Shamshudeen Usman, Dr. Jelani Aliyu wadanda suke haskawa a duniya. Kenan da a ce za a kawo wadannan cikin tsarin shugabancinmu na siyasa a cikin gida, me za su zama? Wannan tambaya ce da ta cancanci a bai wa wanda ya amsa kyautar Naira Miliyan Daya. Kuma amsar mai sauki ce, ita ce: za su samar da sarari da kuma shimfida aiki na ci gaba kamar yadda yake a kasashen duniya tare da tabbatar da shugabanci nagari.

Ma’aikatan gwamnati marasa cancanta ba su komai illa wargaza tsari da ci gaba wadanda suke zama karfen-kafa masu hana ruwa gudu da bata ruwa ba don su sha ba. Tabbas matukar muna bukatar samun ci gaba, to dole ne mu samo sahihan ma’aikata da suka cancanta amma ba wadanda kaddara ce ta kawo su ba kawai!

Amb. Abraham James, daga Kamfanin Harkokin Sadarwa da Labarai na Hallbibe. Email: [email protected].

Ma'aikaci
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
An Jinjinawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Karfafa Tsarin Kiwon Lafiya A Afirka

An Jinjinawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Karfafa Tsarin Kiwon Lafiya A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.