• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Neman Haifar Da Baraka A Yankin Taiwan Jigo Ne Na Illata Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabar Tekun Taiwan

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Neman Haifar Da Baraka A Yankin Taiwan Jigo Ne Na Illata Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabar Tekun Taiwan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban jami’in yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te, ya gabatar da jawabi a ranar Alhamis 10 ga watan nan, inda ya sake bayyana ra’ayin cewa wai bangarori biyu na gabar tekun Taiwan ba su da alaka da juna, da sabon ra’ayin kasancewar kasashe biyu, wanda hakan ya kasance karya ta neman ware yankin Taiwan daga babban yankin Sin, da zummar yayata ra’ayin kawo baraka, da zuga wutar yin fito-na-fito tsakaninsu. To sai dai kuma ikirarin nasa ba zai sauya ainihin gaskiya ba, wato yankin Taiwan wani sashi ne na kasar Sin.

 

“Sanawar Alkahira” da aka fitar a shekarar 1943, da “Sanarwar Potsdam” da aka sanar a shekarar 1945, dukkansu na tabbatar da cewa, Japan ta mayar wa kasar Sin yankin Taiwan da ta mamaye. Kuma hakan ya kasance muhimmin tushe na wanzar da doka da oda bayan Yakin Duniya na biyu, wanda kuma ya aza tubali a bangaren kare doka, don tabbatar da cewa yankin Taiwan ya kasance sashin kasar Sin da ba za a iya ware shi ba.

  • Majalisar Tarayya Ta Samar Da Naira Biliyan 24 Domin Gyara Filin Jiragen Sama Na Kebbi Da Nasarawa
  • MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

Yau shekaru 53 da suka gabata, a gun babban taron MDD karo na 26, an zartas da kuduri mai lamba 2,758, bisa kuri’un amincewa mafiya rinjaye, don mayar da ikon kasar Sin a majalisar, inda aka amince da cewa, wakilin gwamnatin babban yankin Sin kadai ne ke iya wakiltar kasar Sin a majalisar, kana an kori wakilin yankin Taiwan daga majalisar da sauran hukumomin MDD masu nasaba.

 

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

A cikin rabin karnin da ya gabata, majalisar da sauran hukumomin MDD, da kungiyoyin kasa da kasa, sun nace ga wannan kuduri ba tare da tangarda ba. Sin ta kuma kulla dangantakar diplomasiyya tsakaninta da sauran kasashe 183 bisa ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Abin da ya alamta cewa, nacewa ga wannan ka’ida, matsaya ce daya tak a duniya baki daya, wadda ba wanda zai iya canja shi ta.

 

Makomar yankin Taiwan na dogaro da dinkewar kasar Sin, kuma farfadowar al’ummar Sinawa na amfanar al’ummun yankin Taiwan. A daya hannu, yunkurin masu neman kawo baraka kamar yadda Lai Ching-te yake yi za su ci tura. Dinkewar kasar Sin sha’ani ne da ba shakka zai tabbata, kuma ba wanda zai iya hana aukuwarsa. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Murnar Cika Shekaru 10 Da Kafuwar Huldar Abota Bisa Manyan Tsare-Tsare A Duk Fannoni Tsakanin Sin Da Jamus

Next Post

Ɗan Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Ya Rasu

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

2 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

4 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

4 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

8 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

10 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

10 hours ago
Next Post
Ɗan Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Ya Rasu

Ɗan Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.