• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Neman Haifar Da Baraka A Yankin Taiwan Jigo Ne Na Illata Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabar Tekun Taiwan

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Neman Haifar Da Baraka A Yankin Taiwan Jigo Ne Na Illata Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabar Tekun Taiwan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban jami’in yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te, ya gabatar da jawabi a ranar Alhamis 10 ga watan nan, inda ya sake bayyana ra’ayin cewa wai bangarori biyu na gabar tekun Taiwan ba su da alaka da juna, da sabon ra’ayin kasancewar kasashe biyu, wanda hakan ya kasance karya ta neman ware yankin Taiwan daga babban yankin Sin, da zummar yayata ra’ayin kawo baraka, da zuga wutar yin fito-na-fito tsakaninsu. To sai dai kuma ikirarin nasa ba zai sauya ainihin gaskiya ba, wato yankin Taiwan wani sashi ne na kasar Sin.

 

“Sanawar Alkahira” da aka fitar a shekarar 1943, da “Sanarwar Potsdam” da aka sanar a shekarar 1945, dukkansu na tabbatar da cewa, Japan ta mayar wa kasar Sin yankin Taiwan da ta mamaye. Kuma hakan ya kasance muhimmin tushe na wanzar da doka da oda bayan Yakin Duniya na biyu, wanda kuma ya aza tubali a bangaren kare doka, don tabbatar da cewa yankin Taiwan ya kasance sashin kasar Sin da ba za a iya ware shi ba.

  • Majalisar Tarayya Ta Samar Da Naira Biliyan 24 Domin Gyara Filin Jiragen Sama Na Kebbi Da Nasarawa
  • MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

Yau shekaru 53 da suka gabata, a gun babban taron MDD karo na 26, an zartas da kuduri mai lamba 2,758, bisa kuri’un amincewa mafiya rinjaye, don mayar da ikon kasar Sin a majalisar, inda aka amince da cewa, wakilin gwamnatin babban yankin Sin kadai ne ke iya wakiltar kasar Sin a majalisar, kana an kori wakilin yankin Taiwan daga majalisar da sauran hukumomin MDD masu nasaba.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

A cikin rabin karnin da ya gabata, majalisar da sauran hukumomin MDD, da kungiyoyin kasa da kasa, sun nace ga wannan kuduri ba tare da tangarda ba. Sin ta kuma kulla dangantakar diplomasiyya tsakaninta da sauran kasashe 183 bisa ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Abin da ya alamta cewa, nacewa ga wannan ka’ida, matsaya ce daya tak a duniya baki daya, wadda ba wanda zai iya canja shi ta.

 

Makomar yankin Taiwan na dogaro da dinkewar kasar Sin, kuma farfadowar al’ummar Sinawa na amfanar al’ummun yankin Taiwan. A daya hannu, yunkurin masu neman kawo baraka kamar yadda Lai Ching-te yake yi za su ci tura. Dinkewar kasar Sin sha’ani ne da ba shakka zai tabbata, kuma ba wanda zai iya hana aukuwarsa. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Murnar Cika Shekaru 10 Da Kafuwar Huldar Abota Bisa Manyan Tsare-Tsare A Duk Fannoni Tsakanin Sin Da Jamus

Next Post

Ɗan Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Ya Rasu

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

10 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

11 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

12 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

13 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

14 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

16 hours ago
Next Post
Ɗan Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Ya Rasu

Ɗan Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.