• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

byBello Hamza
12 months ago
Buratai

Gidauniyar TY Burutai ta mika sakon taya murna ga Kwamanda Tunde Giwa Daramola kan zama shugaban kungiyar masu tseren kwale kwale ta Jihar Ondo.

Wanda Gwamnan jihar wato Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya nada shi. Sakon taya murnar ta fito ne ta hannun Shugaban Gidauniyar, Ibrahim Dahiru Danfulani Sadaukin Gwarkuwan Keffi/Betara Biu wanda ya mika wa manema labarai.

  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin
  • Xi Ya Amsa Wasikar Wakilan Daliban Da Suka Halarci Gasar Kere-Keren Kimiyya Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin

Kwamanda Tunde Giwa Daramola mai ritaya mutum ne da ya yi fice daga cikin tsarraraki kuma babban abin alfahrin dalban makarantar sojoji da ke Kaduna aji na 29. Ba kawai babban soja ba ne ya kuma kasance kwararren ma’aikaci. Yanayin tafiyar da al’amuran shi da kuma maida hankali wajen aiki da kuma wasannin motsa jiki ya zamar dashi wanda ya cancanci wannan mukami.

Uban Gidauniyar TY Burutai, wato Ambasada Janar Tukur Yusuf Buratai tsowan shugaban sojojin Nijeriya ya yi matukar murna da jin dadi game da wannan nadin da a ka yi ma Kwamanda Giwa Daramola.

Ya Kuma jadadda muhimmancin samun shugaba kamar Giwa Daramola a shugabancin wannan kungiya. A cewar sa; “Kwamanda Giwa Daramola yana da ruhin dagiya da kwarewa a harkar motsa jiki wanda matasan mu suke bukata a matsayin abin koyi” Ya kara da cewa “Kwarewar shi da kuma maida hankalin shi ga ci gaba ba bu shakka zai daga Kungiyar zuwa matakin da ya kamata”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Gidauniyar tana alfahari da tallafa wa shugabanni kaman Kwamanda Giwa Daramola wanda suka tsayu da gaskiya da rikon amana a wajen aiki. Muna da yakini karkashin jagorancinshi na Shugaban kungiyar Masu Tseren Kwale kwale Na Jihar Ondo zai samar da ci gaba da sabbin masu wasannin motsa jiki a fadin jihar.

Muna jinjina wa gwamnatin jihar Ondo a kan wannan nadi inda gwamnan yayi duba da kwarewa a harkar tsaro da kuma kokari a fannin motsa jiki wajen wannan nadin. Gidauniyar TY Buratai ta shirya tsaf domin ganin irin ci gaban da za a samu karkashin shugabancin Kwamanda Giwa Daramola a jihar baki daya.

A halin yanzu yabo da jinjina sai kara fitowa yake yi ga shugaban kasa Tinubu a kan yadda ya dauki sashen samar da wutar lantarki a Nijeriya da matukar muhimmanci. Yabo na baya-bayan nan ya fito daga wata kallabi a tsakanin rawunna, Injiniya Amina Ahmed a yayin babban taron makashi na kasa da aka yi a garin Legas a makon jiya.

Taron ya tara masana daga sasan kasar inda aka tatauna yadda za a bunkaasa hanyoyin samar da makashi ga al’ummar Nijeriya gaba daya

Ta bayyana cewa, samar da cikakken wutar lantarki zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin al’umma. Ta ce, bunkasa hanyoyin samar da lantarki ta hanyar hasken rana, zai taimaka wajen bunkasa sana’o’in al’ummar karkara.

Daga nan kuma Injiniya Amina Ahmed ta yi kira gan mata musamman na karkara da su nemi Ilimi tare da rike sana’a, “Ba sai sun nemi sana’a ko aikin gwamnati ba, domin a wannan zamanin, gwamnmati ba za ta iya samar wa da al’umma aiki gaba daya ba, a kan haka ta nemi sauran al’umma musamman masu hannu da shuni da su rika tallafa wa matasan da ke unguwanni ko garuruwansu da shawarwari da kuma tallafi don su samu dogaro da kawunansu.

Daga karshe ta yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a kan yadda ya dauki lamarin samar da wutar lantarki da matukar muhimanci. Za a iya lura da haka ne ta hanyar da ya zabi wadanda suke jagorantar ma’aikatar wutar lantarki musamman Minista Hon Adebayo Adelabu, ‘Hon Adebayo Adelabu ya jajirce wajen tattabar da an tsaftace harkar bayar da wutar lantarki a Nijeriya, in ji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
Next Post
Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi

Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC - Kwamishinan Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version