• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma

by Sulaiman
12 months ago
Arewa maso Yamma

Ministan tsaro, Mohammed Abubakar, a daren ranar Alhamis ya sake jaddada aniyar gwamnatin tarayya na magance matsalar ‘yan bindiga da kuma rashin tsaro a fadin Nijeriya baki daya.

 

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai wa Gwamna Uba Sani ziyara a gidan gwamnatin Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna a wani rangadin da ya ke yi a shiyyar Arewa maso Yamma.

  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 20 Da Kafa Cikakkiyar Dangantakar Abokantaka Bisa Manyan Tsare-tsare Tsakanin Sin Da Italiya A Milan
  • A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Ziyarar dai na da nufin kammala shirye-shiryen kaddamar da shirin ‘Operation Fansar Yamma,’ rundunar hadin gwiwa ta rundunar soji da aka kafa domin magance matsalar rashin tsaro a yankin.

 

LABARAI MASU NASABA

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Abubakar, a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala ziyarar, ya jaddada kafa cibiyar gudanarwar tsaro a shiyyar Arewa maso Yamma a matsayin wani muhimmin mataki na magance matsalar ‘yan bindiga da suka addabi yankin.

 

Ministan ya kuma bayyana irin kokarin da gwamnatin kasar ke yi na hadin gwiwa da kasashe makwabta musamman jamhuriyar Nijar wajen yaki da ta’addanci da safarar makamai.

 

A nasa jawabin, a lokacin da yake maraba da Ministan, Gwamna Sani ya jaddada bukatar hadin kan shugabannin yankin domin magance matsalar rashin tsaro.

 

Gwamna Sani ya nuna godiya ga gwamnatin tarayya bisa jajircewar da ta yi na ganin ta magance matsalolin rashin tsaro da ke addabar shiyyar Arewa maso Yamma.

 

Ya kuma bayyana damuwarsa kan illar rashin tsaro a shiyyar Arewa maso Yamma, da suka hada da karancin abinci, karancin hanyoyin kiwon lafiya, da karuwar talauci.

 

Sai dai gwamnan ya bayyana fatansa na cewa, shirin “Operation Fansar Yamma” wanda ake shirin kaddamarwa, zai samar da yanayin zuba jari da bunkasar tattalin arziki a yankin.

 

Gwamnan ya kuma bayar da shawarar mayar da ‘Operation Safe Haven’ da ke Kudancin Kaduna zuwa shiyya ta 1 da ke Kaduna maimakon shiyya ta uku da ke Jos a Jihar Filato domin samun saukin gudanar da ayyuka.

 

Ya yaba da goyon bayan da shugaban kasa Bola Tinubu ke yi bai wa shiyyar Arewa maso Yamma, ya kuma nuna godiya ga Ministan Tsaro, Shugaban Hafsan Tsaro, da Babban Hafsan Soja bisa goyon bayan da suke bai wa yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe
Labarai

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Next Post
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.